DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Ambaliyar ruwa ta dai-daita mutane 17,000 a Kaduna da Katsina – NEMA

-

Hukumar bayar da agajin gaggawa ta Nijeriya NEMA ta bayyana cewa akalla mutane 17,000 ne ambaliyar ruwa ta raba da muhallansu a jihohin Kaduna da Katsina cikin shekarar 2025.

 

Google search engine

Wannan bayani ya fito daga bakin shugaban ofishin hukumar na jihar Kaduna Suleiman Muhammad, yayin gudanar da aikin bibiyar yankunan da lamarin ya shafa.

 

A cewar Suleiman, irin asarar da aka samu ta tilasta hukumar yin aiki tare da sauran masu ruwa da tsaki wajen gudanar da ayyukan ceto da kuma na tallafi don rage radadi.

 

Kazalika ya bayyana samun rahoton asarar rai a jihar Katsina sakamakon ambaliyar, sai dai ba a samu asarar rai a Kaduna ba.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Dan majalisar wakilan Nijeriya ya sauys sheka daga PDP zuwa ADC

Dan majalisar tarayya mai wakiltar mazabar Tambuwal/Kebbe a jihar Sokoto, Abdussamad Dasuki ya sanar da ficewarsa daga jam’iyyar PDP, inda ya koma ADC. A cikin wasiƙar...

Sanata Wamako ya raba wa marayu su 10,000 tallafin N1,000 kowane a jihar Sokoto

Tsohon gwamnan jihar Sokoto kuma Sanata mai wakiltar Sokoto ta Arewa, Aliyu Magatakarda Wamakko, ya bayar da tallafin miliyan 10, ga mutane dubu 10 da...

Mafi Shahara