Gwamnan jihar Osun Ademola Adeleke ya sanar da ficewarsa daga jam‘iyyar PDP, yana mai bayyana rigingimun cikin gida a matsayin dalilin daukar matakin.
Cikin wata sanarwa da ya wallafa a shafinsa na sada zumunta, gwamna Adeleke ya tabbatar da cewa ya mika takardar ficewar ga masu ruwa da tsaki na jam’iyyar a jihar tasa.
Jaridar Punch ta ruwaito cewa ficewar ta zo ne sa’o’i kadan bayan da aka yi hasashen cewa gwamnan ba zai sake neman tsayawa takara a jam’iyyar ba, har sai an shawo kan matsalolin da jam’iyyar ke fuskanta a tsakar gidanta na siyasa.



