DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Gwamnan Osun Adeleke ya fice daga jam’iyyar PDP

-

Gwamnan jihar Osun Ademola Adeleke ya sanar da ficewarsa daga jam‘iyyar PDP, yana mai bayyana rigingimun cikin gida a matsayin dalilin daukar matakin.

 

Google search engine

Cikin wata sanarwa da ya wallafa a shafinsa na sada zumunta, gwamna Adeleke ya tabbatar da cewa ya mika takardar ficewar ga masu ruwa da tsaki na jam’iyyar a jihar tasa.

 

Jaridar Punch ta ruwaito cewa ficewar ta zo ne sa’o’i kadan bayan da aka yi hasashen cewa gwamnan ba zai sake neman tsayawa takara a jam’iyyar ba, har sai an shawo kan matsalolin da jam’iyyar ke fuskanta a tsakar gidanta na siyasa.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Har yanzu bamu kammala bincike ba shiyasa bamu gurfanar da El-rufa’i a gaban kotu ba – EFCC

Hukumar EFCC, mai yaki a cin hanci da rashawa a Nijeriya ta bayyana dalilin da ya sa har yanzu ba ta kai tsohon gwamnan Kaduna,...

Wanene sabon Shugaban Rundunar ‘Yan Sandan Nijeriya, Olatunji Disu?

AIG Olatunji Disu ya kasance gogaggen jami’i wanda aka nada don jagorantar rundunar 'yan sandan kasar a matsayin IGP na 23. A cewar fadar shugaban...

Mafi Shahara