DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Gwamnonin Arewa za su tara Naira biliyan 228 don yakar matsalar tsaro

-

Gwamnonin Arewa da sarakunan gargajiya sun bukaci a dakatar da hakar ma’adanai a yankin na tsawon watanni shida, suna bayyana shi a matsayin babban dalilin ta’azzarar matsalolin tsaro a yankin.

 

Google search engine

Wannan ya biyo bayan wani taro da suka gudanar a ranar Litinin, domin tattaunawa kan yadda za a shawo kan matsalar.

 

Kazalika sun bayyana shirin bude asusu wanda za su tara Naira biliyan 228 don inganta yakinsu da matsalar.

 

Karkashin shirin dai, kowace jiha da kananan hukumominta za su rika bayar da Naira biliyan 1 a kowane wata, kamar yadda jaridar Punch ta ruwaito.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Fadar Shugaba Tinubu ta soki Atiku kan kwatanta gwamnatinsa da ta mulkin soja

Fadar Shugaban Nijeriya ta caccaki madugun adawa Atiku Abubakar, bisa kwatanta gwamnatin Tinubu da mulkin soja, tana mai bayyana kalaman nasa a matsayin abinda basu...

Majalisar Dattawa ta dakatar da muhawara kan gyaran dokar zabe tare da shiga zaman sirri

Majalisar Dattawan Nijeriya ta dakatar da muhawarar kan kudirin dokar zaɓe ta 2022, domin bai wa ’yan majalisa damar yin nazari mai zurfi kafin ɗaukar...

Mafi Shahara