DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Wike na rikewa Tinubu duk filin da gwamnati ta kwace a Abuja – Hadiminsa

-

Hadimi ga ministan Abuja Nyesom Wike, Lere Olayinka ya bayyana cewa duk wani fili da gwamnati ta kwace iko da mallakarsa a birnin na kasancewa a hannun ministan ne cikin aminci don ya rikewa shugaban Nijeriya Bola Tinubu.

Olayinka ya bayyana haka ne yayin wata hira da gidan talabijin na Arise, yana mai cewa a halin yanzu akwai filaye akalla 1000 da aka kwace ikon mallakar tasu, kamar yadda jaridar Punch ta ruwaito.

Google search engine

Ya bayyana cewa kwacewar na zuwa ne sakamakon rashin bin ka’idoji ko kuma biyan wasu hakkoki daga mamallakansu.

Ya kara da jaddada cewa duk wanda ya karya doka, tabbas za ta yi aiki a kansa.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Har yanzu bamu kammala bincike ba shiyasa bamu gurfanar da El-rufa’i a gaban kotu ba – EFCC

Hukumar EFCC, mai yaki a cin hanci da rashawa a Nijeriya ta bayyana dalilin da ya sa har yanzu ba ta kai tsohon gwamnan Kaduna,...

Wanene sabon Shugaban Rundunar ‘Yan Sandan Nijeriya, Olatunji Disu?

AIG Olatunji Disu ya kasance gogaggen jami’i wanda aka nada don jagorantar rundunar 'yan sandan kasar a matsayin IGP na 23. A cewar fadar shugaban...

Mafi Shahara