DCL Hausa Radio
Kaitsaye

‘Yan bindiga sun sace manoma 11 a jihar Kaduna

-

An samu tashin hankali a Unguwan Nungu da ke mazabar Bokana a karamar hukumar Sanga da ke jihar Kaduna, bayan da ‘yan bindiga suka sace mutane 11 a lokacin da suke dawowa daga gonakinsu.

 

Google search engine

Daily Trust ta ruwaito mazauna yankin na tabbatar da cewa ‘yan bindigar sun yi awon gaba da mutanen cikin dazuka, ba tare da an san ina suka nufa ba.

 

Kazalika wani mazaunin yankin da ya bukaci a sakaya sunansa ya bayyana cewa ‘yan bindigar sun nemi a biya su kudin fansa miliyan 11 kafin su sako mutanen da suka sace.

 

Rahotanni sun nuna cewa lamarin ya ta’azzara fargaba a zukatan mazauna yankin da kuma masu makwabtaka da su.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Fadar Shugaba Tinubu ta soki Atiku kan kwatanta gwamnatinsa da ta mulkin soja

Fadar Shugaban Nijeriya ta caccaki madugun adawa Atiku Abubakar, bisa kwatanta gwamnatin Tinubu da mulkin soja, tana mai bayyana kalaman nasa a matsayin abinda basu...

Majalisar Dattawa ta dakatar da muhawara kan gyaran dokar zabe tare da shiga zaman sirri

Majalisar Dattawan Nijeriya ta dakatar da muhawarar kan kudirin dokar zaɓe ta 2022, domin bai wa ’yan majalisa damar yin nazari mai zurfi kafin ɗaukar...

Mafi Shahara