DCL Hausa Radio
Kaitsaye

‘Yan bindiga sun sace manoma 11 a jihar Kaduna

-

An samu tashin hankali a Unguwan Nungu da ke mazabar Bokana a karamar hukumar Sanga da ke jihar Kaduna, bayan da ‘yan bindiga suka sace mutane 11 a lokacin da suke dawowa daga gonakinsu.

 

Google search engine

Daily Trust ta ruwaito mazauna yankin na tabbatar da cewa ‘yan bindigar sun yi awon gaba da mutanen cikin dazuka, ba tare da an san ina suka nufa ba.

 

Kazalika wani mazaunin yankin da ya bukaci a sakaya sunansa ya bayyana cewa ‘yan bindigar sun nemi a biya su kudin fansa miliyan 11 kafin su sako mutanen da suka sace.

 

Rahotanni sun nuna cewa lamarin ya ta’azzara fargaba a zukatan mazauna yankin da kuma masu makwabtaka da su.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Dan majalisar wakilan Nijeriya ya sauys sheka daga PDP zuwa ADC

Dan majalisar tarayya mai wakiltar mazabar Tambuwal/Kebbe a jihar Sokoto, Abdussamad Dasuki ya sanar da ficewarsa daga jam’iyyar PDP, inda ya koma ADC. A cikin wasiƙar...

Sanata Wamako ya raba wa marayu su 10,000 tallafin N1,000 kowane a jihar Sokoto

Tsohon gwamnan jihar Sokoto kuma Sanata mai wakiltar Sokoto ta Arewa, Aliyu Magatakarda Wamakko, ya bayar da tallafin miliyan 10, ga mutane dubu 10 da...

Mafi Shahara