DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Gwamnatin Tinubu ba ta tattaunawa da ‘yan bindiga – Daniel Bwala

-

Hadimin shugaban Nijeriya Bola Tinubu, Daniel Bwala, ya jaddada cewa gwamnatin tarayya ba ta taɓa yin tattaunawa da ’yan ta’adda ko biyan su kuɗin fansa ba, duk da jita-jitar da ke yawo game da sakin yara ‘yan makaranta da aka sace.

 

Google search engine

A yayin wata tattaunawa da gidan talabijin na Channels a ranar Laraba, Bwala ya bayyana cewa a wasu gwamnatoci da suka gabata, hukumomi na shiga tattaunawa da’ yan bindiga domin kare rayukan ’yan ƙasa, kamar yadda jaridar Punch ta ruwaito.

 

Sai dai ya ce gwamnatin Tinubu ba ta amince da daukar hanyar ba, domin a cewarsa hakan na kara karfafar ‘yan ta’adda ne a fakaice.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Ƴan kwangila sun girke akwatin gawa a ofishin ma’aikatar kuɗin Nijeriya

‘Yan kwangila sun girke akwatin gawa a kofar shiga ofishin ma’aikatar kudin Nijeriya da ke Abuja.   ‘Yan kwangilar, karkashin inuwar kungiyarsu ta 'yan asalin Nijeriya sun...

Kudin tikitin jiragen sama a wasu sassan Nijeriya ya haura Naira 300,000 – Punch

Wani bincike da jaridar Punch ta gabatar, ya nuna cewa kudin tikitin jiragen sama a wasu sassan Nijeriya ya zarta Naira 300,000.   Binciken ya nuna cewa...

Mafi Shahara