DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Gwamnatin Tinubu ba ta tattaunawa da ‘yan bindiga – Daniel Bwala

-

Hadimin shugaban Nijeriya Bola Tinubu, Daniel Bwala, ya jaddada cewa gwamnatin tarayya ba ta taɓa yin tattaunawa da ’yan ta’adda ko biyan su kuɗin fansa ba, duk da jita-jitar da ke yawo game da sakin yara ‘yan makaranta da aka sace.

 

Google search engine

A yayin wata tattaunawa da gidan talabijin na Channels a ranar Laraba, Bwala ya bayyana cewa a wasu gwamnatoci da suka gabata, hukumomi na shiga tattaunawa da’ yan bindiga domin kare rayukan ’yan ƙasa, kamar yadda jaridar Punch ta ruwaito.

 

Sai dai ya ce gwamnatin Tinubu ba ta amince da daukar hanyar ba, domin a cewarsa hakan na kara karfafar ‘yan ta’adda ne a fakaice.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Har yanzu bamu kammala bincike ba shiyasa bamu gurfanar da El-rufa’i a gaban kotu ba – EFCC

Hukumar EFCC, mai yaki a cin hanci da rashawa a Nijeriya ta bayyana dalilin da ya sa har yanzu ba ta kai tsohon gwamnan Kaduna,...

Wanene sabon Shugaban Rundunar ‘Yan Sandan Nijeriya, Olatunji Disu?

AIG Olatunji Disu ya kasance gogaggen jami’i wanda aka nada don jagorantar rundunar 'yan sandan kasar a matsayin IGP na 23. A cewar fadar shugaban...

Mafi Shahara