DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Gwamnan jihar Zamfara ya gabatar da kasafin kudi N861bn na 2026 ga majalisar dokokin jihar

-

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya gabatar da kasafin kuɗi na Naira biliyan 861 na shekarar 2026 a gaban majalisar dokokin Jihar a Gusau, yana mai cewa wannan kasafi taswira ce ta sauyi, domin a cewarsa, kasafin ya kunshi kuɗin ayyukan ci-gaba na N714bn wanda ya kunshi kaso 83 da kuɗin gudanarwa na kusan N147bn (kaso 17).

Dauda ya ce gwamnatinsa, wadda aka zaɓa a kan alkawarin ceto, gyara da farfaɗo da jihar, ta yi aiki tukuru don farfaɗo da muhimman bangarori da kuma gina tubalin ci-gaba mai ɗorewa.

Google search engine

Hakazalika, Gwamna Lawal ya kara da cewa mutanen Zamfara yanzu suna ganin haske da ci-gaba, yayin da kasafin 2026 wanda ya kira kasafin tabbatar da daidaito da ci-gaba ke nufin zurfafa nasarorin da aka cimma ta hanyar shirin Six-Point Rescue Agenda.

Kasafin ya ba da fifiko ga tsaro, inganta aikin noma, sabunta fannin kiwon lafiya, faɗaɗa ilimi, gina manyan ayyukan raya ƙasa, da kuma ƙarfafa matasa, mata da marasa galihu, tare da tabbatar da cewa babu wani yanki ko al’umma da za a bari a baya.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Shugaba Tinubu ya aika da sunan Dambazau domin tantancewa a matsayin jaakada

Shugaba Bola Tinubu ya ya aike da tsohon ministan cikin gida, Abdulrahman Dambazau, wanda ya taba zama shugaban sojin ƙasa, a matsayin jakada domin tantancewa...

Amurka ta ba da tallafin Dala miliyan 5 domin ceto yara masu fama da tamowa a Nijeriya

Kasar Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 5 ga asusun kula da yara na majalisar dinkin duniya (UNICEF) domin kai agajin gaggawa ga yara...

Mafi Shahara