DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Sojoji sun ceto mutane 318 da aka sace tare da kama 74 da ake zargi da hannu – Hedkwatar tsaron Nijeriya

-

Rundunar tsaron Nijeriya ta bayyana cewa dakarun da ke aiki a sassa daban-daban na ƙasar sun ceto mutane 318 da aka yi garkuwa da su a watan Nuwamba, tare da kama wasu 74 da ake zargi da ta’addanci da fataucin mai da sauran laifuka.

A cewar Daraktan yada labarai na tsaro, Maj. Janar Michael Onoja, wanda ya yi jawabi an Abuja, ya ce a wannan watan kuma ’yan ta’adda 69 da iyalansu sun mika wuya a Arewa maso Gabas.

Google search engine

Hedkwatan tsaron ta ce dakarun sun kuma dakile satar mai da kimar ta kai sama da N217m, tare da rushe wuraren tace mai na bogi 16 da gano lita 201,700 na ɗanyen mai da lita 88,177 na dizal.

Onoja ya kuma yaba wa dakarun bisa ƙoƙarinsu, tare da roƙon jama’a da su ci-gaba da ba da sahihan bayanai ga hukumomin tsaro.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Har yanzu bamu kammala bincike ba shiyasa bamu gurfanar da El-rufa’i a gaban kotu ba – EFCC

Hukumar EFCC, mai yaki a cin hanci da rashawa a Nijeriya ta bayyana dalilin da ya sa har yanzu ba ta kai tsohon gwamnan Kaduna,...

Wanene sabon Shugaban Rundunar ‘Yan Sandan Nijeriya, Olatunji Disu?

AIG Olatunji Disu ya kasance gogaggen jami’i wanda aka nada don jagorantar rundunar 'yan sandan kasar a matsayin IGP na 23. A cewar fadar shugaban...

Mafi Shahara