’Yan majalisar dokokin jihar Zamfara biyu sun fice daga jam’iyyar APC, suna zargin tana fama da rikice-rikice da matsalolin jagoranci.
Shamsudeen Hassan Basko na Talata-Mafara Arewa da Nura Dahiru na Birnin-Magaji sun sanar da ficewarsu a cikin takardun murabus da aka karanta a gaban majalisa.
Hassan ya ce rabuwar kawuna, raunin jagoranci da wariya ga ’yan jam’iyya a matakan jiha da kananan hukumomi ne suka sa ya daina tafiyar APC, yana mai cewa hakan bai dace da alkiblarsa da muradin mazabarsa ba.
Dahiru wanda ya koma jam’iyyar PDP, ya ce barin jam’iyyar zai ba shi damar aikin da ya fi dacewa da bukatun mutanen da yake wakilta.
Dukkan su sun gode wa jam’iyyar kan damar da suka samu, tare da bukatar a dauki takardunsu a matsayin cikakken ficewa.



