DCL Hausa Radio
Kaitsaye

‘Yan majalisar dokokin jihar Zamfara biyu sun fice daga jam’iyyar APC

-

’Yan majalisar dokokin jihar Zamfara biyu sun fice daga jam’iyyar APC, suna zargin tana fama da rikice-rikice da matsalolin jagoranci.

Shamsudeen Hassan Basko na Talata-Mafara Arewa da Nura Dahiru na Birnin-Magaji sun sanar da ficewarsu a cikin takardun murabus da aka karanta a gaban majalisa.

Google search engine

Hassan ya ce rabuwar kawuna, raunin jagoranci da wariya ga ’yan jam’iyya a matakan jiha da kananan hukumomi ne suka sa ya daina tafiyar APC, yana mai cewa hakan bai dace da alkiblarsa da muradin mazabarsa ba.

Dahiru wanda ya koma jam’iyyar PDP, ya ce barin jam’iyyar zai ba shi damar aikin da ya fi dacewa da bukatun mutanen da yake wakilta.

Dukkan su sun gode wa jam’iyyar kan damar da suka samu, tare da bukatar a dauki takardunsu a matsayin cikakken ficewa.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Har yanzu bamu kammala bincike ba shiyasa bamu gurfanar da El-rufa’i a gaban kotu ba – EFCC

Hukumar EFCC, mai yaki a cin hanci da rashawa a Nijeriya ta bayyana dalilin da ya sa har yanzu ba ta kai tsohon gwamnan Kaduna,...

Wanene sabon Shugaban Rundunar ‘Yan Sandan Nijeriya, Olatunji Disu?

AIG Olatunji Disu ya kasance gogaggen jami’i wanda aka nada don jagorantar rundunar 'yan sandan kasar a matsayin IGP na 23. A cewar fadar shugaban...

Mafi Shahara