DCL Hausa Radio
Kaitsaye

An gurfanar da alkali gaban kotu kan zargin karbar cin hanci a Gombe

-

Wani alkali da ke wata kotun majistire a jihar Gombe, Mohammed Kumo, ya gurfana a gaban kotu kan zargin sa da karbar cin hanci da kuma tatsar kudade.

 

Google search engine

Hukumar EFCC mai yaki da yi wa tattalin arzikin Nijeriya zagon kasa ce ta gurfanar da alkalin, kamar yadda yake a cikin wata sanarwa da ta fitar.

 

Sanarwar ta ce an maka shi ne gaban mai shari’a H.H Kereng da ke babbar kotun Gombe, ana tuhumar sa da aikata laifuka uku, kamar yadda EFCC reshen jihar ta mika.

 

Sai dai wanda ake kara ya musanta aikata laifukan, dalili kenan da mai shari’a ya bayar da belinsa, tare da dage zaman shari’ar zuwa ranakun 13 da 14 ga watan Janairun 2026, kamar yadda jaridar Punch ta ruwaito.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Limaman coci sun musanta zargin kisan Kiristoci a Nijeriya

Wasu limaman coci sun yi watsi da zargin Amurka da ke cewa ana gudanar da kisan kiyashi kan Kiristoci a Nijeriya.   Limaman sun mayar da martani...

Mun kashe Naira 100bn a fannin tsaron Borno cikin 2025 – Gwamna Zulum

Gwamnan jihar Borno Babagana Umara Zulum ya nuna damuwa da yadda ake kashe makuden kudade a fannin tsaro, yana mai cewa gwamnatinsa ta kashe Naira...

Mafi Shahara