DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Limaman coci sun musanta zargin kisan Kiristoci a Nijeriya

-

Wasu limaman coci sun yi watsi da zargin Amurka da ke cewa ana gudanar da kisan kiyashi kan Kiristoci a Nijeriya.

 

Google search engine

Limaman sun mayar da martani ne kan maganganun shugaban Amurka Donald Trump, wanda da fari ya yi barazanar daukar matakin soji a kan kasar.

 

Yayin da yake zantawa da manema labarai a Abuja, Bishop Timothy Cheren, wanda ya jagoranci tawagar, ya ce babu wata hujja da ke nuna cewa akwai kisan kiyashi da gwamnati ke daukar nauyi ko kuma dauke kai daga haka.

 

Cheren ya yabawa kokarin Shugaba Bola Ahmed Tinubu wajen yaki da matsalar tsaro, tare da mika kira ga ‘yan Nijeriya da su mara wa kokarin da ake yi na kawo karshen ta’addanci a Nijeriya, kamar Daily Trust ta ruwaito.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Mun kashe Naira 100bn a fannin tsaron Borno cikin 2025 – Gwamna Zulum

Gwamnan jihar Borno Babagana Umara Zulum ya nuna damuwa da yadda ake kashe makuden kudade a fannin tsaro, yana mai cewa gwamnatinsa ta kashe Naira...

An gurfanar da alkali gaban kotu kan zargin karbar cin hanci a Gombe

Wani alkali da ke wata kotun majistire a jihar Gombe, Mohammed Kumo, ya gurfana a gaban kotu kan zargin sa da karbar cin hanci da...

Mafi Shahara