DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Limaman coci sun musanta zargin kisan Kiristoci a Nijeriya

-

Wasu limaman coci sun yi watsi da zargin Amurka da ke cewa ana gudanar da kisan kiyashi kan Kiristoci a Nijeriya.

 

Google search engine

Limaman sun mayar da martani ne kan maganganun shugaban Amurka Donald Trump, wanda da fari ya yi barazanar daukar matakin soji a kan kasar.

 

Yayin da yake zantawa da manema labarai a Abuja, Bishop Timothy Cheren, wanda ya jagoranci tawagar, ya ce babu wata hujja da ke nuna cewa akwai kisan kiyashi da gwamnati ke daukar nauyi ko kuma dauke kai daga haka.

 

Cheren ya yabawa kokarin Shugaba Bola Ahmed Tinubu wajen yaki da matsalar tsaro, tare da mika kira ga ‘yan Nijeriya da su mara wa kokarin da ake yi na kawo karshen ta’addanci a Nijeriya, kamar Daily Trust ta ruwaito.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Dan majalisar wakilan Nijeriya ya sauys sheka daga PDP zuwa ADC

Dan majalisar tarayya mai wakiltar mazabar Tambuwal/Kebbe a jihar Sokoto, Abdussamad Dasuki ya sanar da ficewarsa daga jam’iyyar PDP, inda ya koma ADC. A cikin wasiƙar...

Sanata Wamako ya raba wa marayu su 10,000 tallafin N1,000 kowane a jihar Sokoto

Tsohon gwamnan jihar Sokoto kuma Sanata mai wakiltar Sokoto ta Arewa, Aliyu Magatakarda Wamakko, ya bayar da tallafin miliyan 10, ga mutane dubu 10 da...

Mafi Shahara