DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Malami ya musanta zargin daukar nauyin ta’addanci

-

Tsohon Babban Lauyan Nijeriya, Abubakar Malami (SAN), ya musanta zarge-zargen da ke danganta shi da daukar nauyin ta’addanci, yana mai cewa zargin ba su da tushe kuma siyasa ce kawai ake yi da sunansa.

A wata sanarwa da ya fitar ranar Juma’a, Malami ya ce hankalinsa ya kai kan wani rubutu da ke nuni da cewa shi da wasu mutane suna da alaka da wadanda ake zargi da ta’addanci ko taimaka wa masu aikata laifin.

Google search engine

Jaridar Punch ta ruwaito cewa tsohon ministan ya bayyana wadannan zarge-zarge a matsayin “ba su da tushe, balle makama.”

Ya ce ba a taba gayyatar sa, bincike ko kuma tuhumarsa ta kowace hanya daga wata hukuma ta tsaro a cikin gida ko waje ba kan batun daukar nauyin ta’addanci.

Malami ya jaddada cewa irin wadannan rahotanni na iya bata suna da tayar da hankali, don haka akwai bukatar a yi taka-tsantsan wajen yada bayanai marasa inganci.

Ukashatu Ibrahim Wakili
Ukashatu Ibrahim Wakilihttp://dclhausa.com
Ukashatu Wakili, Mataimakin Babban Edita kuma Mai Kula da Shirin Koyon Sanin Makamar Aiki ne a DCL Hausa. A matsayinsa na ƙwararren ɗan jarida yana tsara ayyukan rediyo da kafafen sada zumunta, fassarar labarai, da tabbatar da sahihancin bayanai. Yana jagorantar shirin horaswa ga masu koyon aiki tare da kula da ingancin rubuce-rubuce da shirye-shiryen gidan jaridar.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Dan majalisar wakilan Nijeriya ya sauys sheka daga PDP zuwa ADC

Dan majalisar tarayya mai wakiltar mazabar Tambuwal/Kebbe a jihar Sokoto, Abdussamad Dasuki ya sanar da ficewarsa daga jam’iyyar PDP, inda ya koma ADC. A cikin wasiƙar...

Sanata Wamako ya raba wa marayu su 10,000 tallafin N1,000 kowane a jihar Sokoto

Tsohon gwamnan jihar Sokoto kuma Sanata mai wakiltar Sokoto ta Arewa, Aliyu Magatakarda Wamakko, ya bayar da tallafin miliyan 10, ga mutane dubu 10 da...

Mafi Shahara