DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Amurka ta fara gamsuwa da matakan Tinubu kan tsaron Nijeriya

-

Dan majalisar wakilan Amurka, Riley Moore, ya yaba wa gwamnatin Najeriya kan ceto yara 100 da aka sace daga St. Mary’s Private Catholic School a Papiri, karamar hukumar Agwara, Jihar Neja.

A cikin wata sanarwa da ya wallafa a shafin X, Moore ya ce wannan ceton yana nuna himma ta gwamnatin Najeriya wajen magance matsalolin tsaro karkashin shugabancin Shugaba Bola Tinubu.

Google search engine

Dan majalisar ya kara da cewa an kafa kwamitin hadin gwiwa tsakanin Amurka da Najeriya don magance zargin tsangwamar Kiristoci a kasar.

Ziyarar Moore ta biyo bayan tattaunawar tsaro tsakanin Mai ba Shugaban Kasa shawara kan tsaro, Nuhu Ribadu, da Sakataren Tsaron Amurka, Pete Hegseth, a Washington a watan Nuwamba, inda aka tattauna zargin tsangwamar Kiristoci a Najeriya.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Har yanzu bamu kammala bincike ba shiyasa bamu gurfanar da El-rufa’i a gaban kotu ba – EFCC

Hukumar EFCC, mai yaki a cin hanci da rashawa a Nijeriya ta bayyana dalilin da ya sa har yanzu ba ta kai tsohon gwamnan Kaduna,...

Wanene sabon Shugaban Rundunar ‘Yan Sandan Nijeriya, Olatunji Disu?

AIG Olatunji Disu ya kasance gogaggen jami’i wanda aka nada don jagorantar rundunar 'yan sandan kasar a matsayin IGP na 23. A cewar fadar shugaban...

Mafi Shahara