DCL Hausa Radio
Kaitsaye

APC ta dage sauya shekar Gwamnan Taraba zuwa Janairun 2026

-

Shugaban jam’iyyar APC na Jihar Taraba, Ibrahim Tukur, ya tabbatar cewa gwamnan jihar, Agbu Kefas, zai sauya sheƙa zuwa APC a hukumance a watan Janairu 2026.

Rahoton gidan talabijin na Channels ya ce an dage sauyin sheƙan da aka tsara ranar 19 ga Nuwamba saboda sace ɗalibai a Jihar Kebbi.

Google search engine

A wani taron manema labarai a Jalingo, Tukur ya ce an ɗauki matakan dakatar da wasu shugabannin ƙananan hukumomi saboda saba wa kundin tsarin jam’iyya, sannan ya nemi sulhu da mabiya maimakon zuwa kotu.

Haka kuma, an soke dakatarwar ɗan majalisar jihar Taraba, Abel Peter, da aka dakatar saboda zargin yin aiki da ya saba wa jam’iyya.

Shugaban jam’iyyar ya kuma yi watsi da ikirarin tsohon mataimakin shugaban ƙasa, Atiku Abubakar, na ɗaukar mulki a Taraba, inda ya ce APC ta riga ta karɓi fadar gwamnatin jihar kuma ba ta da niyyar janyewa.

Sabbin Labarai

Har yanzu bamu kammala bincike ba shiyasa bamu gurfanar da El-rufa’i a gaban kotu ba – EFCC

Hukumar EFCC, mai yaki a cin hanci da rashawa a Nijeriya ta bayyana dalilin da ya sa har yanzu ba ta kai tsohon gwamnan Kaduna,...

Wanene sabon Shugaban Rundunar ‘Yan Sandan Nijeriya, Olatunji Disu?

AIG Olatunji Disu ya kasance gogaggen jami’i wanda aka nada don jagorantar rundunar 'yan sandan kasar a matsayin IGP na 23. A cewar fadar shugaban...

Mafi Shahara