DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Faransa ta samar da kayan aiki wajen dakile yunkurin juyin mulkin Jamhuriyar Benin – Gidan talabijin na France 24

-

Wani hadimin shugaban Faransa ya shaida wa gidan talabijin na France24 cewa Shugaba Emmanuel Macron ya tallafa wajen dakile yunkurin juyin mulkin da aka so yi a Jamhuriyar Benin.

Gidan talabijin din ya ruwaito hadimin Macron din na cewa mai gidansa ya tattauna da shugabannin ECOWAS da suka hada da Najeriya da Saliyo kafin samar da kayan aikin da ake bukata kafin samun damar kakkabe sojojin da suka yi yunkurin juyi9n mulkin. Hadimin shugaban Faransa da ya bukaci kada gidan talabijin na France24 ya bayyana sunansa ya ce tallafin da Faransa ta bayra ga sojojin Jamhuriyar Benin sun hada da bayanan sirri domin tabbatar da cewa juyin mulkin da aka so yi bai yi nasara ba.

Google search engine
Ukashatu Ibrahim Wakili
Ukashatu Ibrahim Wakilihttp://dclhausa.com
Ukashatu Wakili, Mataimakin Babban Edita kuma Mai Kula da Shirin Koyon Sanin Makamar Aiki ne a DCL Hausa. A matsayinsa na ƙwararren ɗan jarida yana tsara ayyukan rediyo da kafafen sada zumunta, fassarar labarai, da tabbatar da sahihancin bayanai. Yana jagorantar shirin horaswa ga masu koyon aiki tare da kula da ingancin rubuce-rubuce da shirye-shiryen gidan jaridar.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Gwamna Zulum zai ba duk dan Borno da ke hijira a Kamaru N500,000

Gwamnan Jihar Borno, Farfesa Babagana Umara Zulum, ya bayyana cewa gwamnatin jiharsa za ta ba kowane ɗan gudun hijira ɗan Borno da yake a Kamaru...

Najeriya da Saudiyya sun rattaba hannu kan yarjejeniyar tsaro

Najeriya da Masarautar Saudiyya sun kulla sabuwar yarjejeniya ta shekaru biyar domin ƙarfafa haɗin gwiwar tsaro da dangantakar soja tsakanin kasashen biyu. A cewar wata sanarwa...

Mafi Shahara