DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Majalisar dattawa ta gayyaci ministan sufurin jiragen sama kan tsadar tikitin jirgi

-

Majalisar Dattawa ta gayyaci Ministan Sufurin Jiragen Sama, Festus Keyamo, da manyan masu ruwa da tsaki a bangaren sufurin jirage domin tattaunawar gaggawa bayan korafe-korafen jama’a game da tsadar tikitin jirgin sama a kasar.

Wannan matakin ya biyo bayan korafin da Sanata Buhari Abdulfatai ya gabatar, inda ya gargadi cewa hauhawar farashin jirgi na iya haifar da matsalar sufuri a fadin kasar, musamman yayin da ake shiga hutun karshen shekara.

Google search engine

A yayin tattaunawar, Sanata Buhari ya ce ‘yan Najeriya na kuka da tsadar jirgin cikin gida da ke kara tashi daga wata zuwa wata.

Ya bayyana cewa tikitin jirgi daga Abuja zuwa Legas yanzu ya kai tsakanin N400,000 zuwa N600,000, wanda ya sanya mutane da dama daina tafiya-tafiye ta sama.

Sanatan daga Jihar Oyo ya kara da cewa abin na kara dagule wa jama’a saboda matsalolin tsaro da wahalar tafiya a manyan hanyoyin mota.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Babu adawa a jihar Plateau a zaben 2027 – Caleb Muftwang

Gwamnan Jihar Plateau, Caleb Manasseh Mutfwang, ya bayyana cewa zuwa zaben 2027 jam’iyyarsa ba za ta samu adawa a jihar ba. Ya fadi hakan ne...

Obasanjo ya musanta rubuta sanarwar mutuwarsa

Tsohon Shugaban Nijeriya, Olusegun Obasanjo, ya musanta wani rubutu da ke yawo a kafafen sada zumunta da ke ikirarin cewa ya fitar da sanarwar mutuwarsa. Rubutun...

Mafi Shahara