DCL Hausa Radio
Kaitsaye

‘Yan sandan Abuja sun cafke mai kai wa ‘yan bindigar Zamfara harsasai

-

Jami’an ‘Yan Sandan Birnin Tarayya sun kama wani mutum mai shekaru 32, Ahmed Abubakar, bisa zargin ƙoƙarin sayar da harsasai guda 1,000 ga ‘yan bindiga a jihar Zamfara.

Kwamishinan ‘Yan Sanda na FCT, Miller G. Dantawaye, ya ce an kama Ahmed ne ranar Litinin da misalin ƙarfe 3:30 na yamma a Unguwar Dodo, Gwagwalada, bayan samun sahihan bayanai.

Google search engine

Jaridar Daily Trust ta ruwaito Bincike ya nuna cewa Ahmed yana hulɗa da wani mai suna Yusuf Mohammed, kuma an aika shi da wannan aikin ne ta hannun ƙanin sa, Ahmed Yakubu, wanda ake kyautata zaton yana da hannu a harkar laifuka kuma har yanzu ba a kama shi ba.

An ce ana ƙoƙarin cafke Yakubu da kuma rushe wannan hanyar laifi baki ɗaya, yayin da Ahmed ke hannun ‘yan sanda a yanzu.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Babu adawa a jihar Plateau a zaben 2027 – Caleb Muftwang

Gwamnan Jihar Plateau, Caleb Manasseh Mutfwang, ya bayyana cewa zuwa zaben 2027 jam’iyyarsa ba za ta samu adawa a jihar ba. Ya fadi hakan ne...

Obasanjo ya musanta rubuta sanarwar mutuwarsa

Tsohon Shugaban Nijeriya, Olusegun Obasanjo, ya musanta wani rubutu da ke yawo a kafafen sada zumunta da ke ikirarin cewa ya fitar da sanarwar mutuwarsa. Rubutun...

Mafi Shahara