Masana harkar soji sun ce rikice-rikicen al’umma ba sa magantuwa da karfin soja kaɗai; sulhu ne babban jigo.
Babban malamin addini Dr. Ahmad Abubakar Gumi ne ya bayyana haka a shafinsa na Facebook inda ya kara da cewa, Minista Bello Matawalle ya fahimci wannan lokacin shugabancinsa a Zamfara, inda kare rayukan jama’a shi ne babban aiki.
Ta hanyar tuntubar bangarorin da ke rikici, ya kusan kawo karshen ta’addanci, inda hanyoyi da kasuwanni suka dawo lafiya kafin rashin hadin kai daga soja ya sake kawo rikici.
Yanzu a matsayinsa na ministan tsaro, Matawalle na amfani da iliminsa wajen kawo zaman lafiya, inda hanya ce da gwamnati ke fatan tabbatar da tsaro, hadin kai, da ci gaba a Nijeriya.



