DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Babu jam’iyyun PDP, ADC a jikin takardar zaben kananan hukumomin da ke gudana a jihar Borno

-

A yayin da masu kada kuri’a a Borno ke zaben shugabancin kananan hukumomi da majalisun tarayya, an lura cewa takardar zabe ba ta dauke da alamomin jam’iyyar PDP da ADC.

Daga farko, jam’iyyun biyu sun bayyana cewa ba za su halarci zaben ranar Asabar ba, sai dai rahoton jaridar Daily Trust daga Maiduguri, Jere da Konduga ya nuna cewa masu kada kuri’a sun yi karanci a wuraren zabe, duk da cewa an fara zabe da karfe 8:00 na safe.

Google search engine

Takardar zaben ta nuna jam’iyyu guda shida kawai: APC, Boot Party, Labour Party (LP), PRP, NNPP da SDP, ba PDP da ADC ba.

Sakataren PDP na Borno, Amos Adziba, ya ce jam’iyyar ta janye daga zaben ne saboda rashin yarda da hukumar zabe da kuma tsadar kudin fom din sha’awa shiga takara da na nadin dan takara.

Shugaban Hukumar Zabe ta jihar Borno, Tahir Shettima, ya ce hukumar na aiki ne bisa doka kuma a muradin dukkan jam’iyyun da suka nuna sha’awa wajen zaben.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Super Eagles ta fara farfado da burinta na zuwa gasar cin kofin duniya ta 2026

Hukumar kwallon kafar Nijeriya ta fara dawo da burin zuwa gasar cin kofin duniya ta 2026 Hukumar Ƙwallon Ƙafa ta Najeriya (NFF) ta shigar da ƙorafi...

Dangote ya shigar da ƙorafi ga hukumar ICPC kan shugaban hukumar NMDPRA

Shugaban Kamfanin Dangote, Aliko Dangote, ya shigar da ƙorafi ga Hukumar ICPC yana zargin Shugaban Hukumar NMDPRA, Farouk Ahmed, da cin hanci da almundahanar kudade. A...

Mafi Shahara