DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Babu jam’iyyun PDP, ADC a jikin takardar zaben kananan hukumomin da ke gudana a jihar Borno

-

A yayin da masu kada kuri’a a Borno ke zaben shugabancin kananan hukumomi da majalisun tarayya, an lura cewa takardar zabe ba ta dauke da alamomin jam’iyyar PDP da ADC.

Daga farko, jam’iyyun biyu sun bayyana cewa ba za su halarci zaben ranar Asabar ba, sai dai rahoton jaridar Daily Trust daga Maiduguri, Jere da Konduga ya nuna cewa masu kada kuri’a sun yi karanci a wuraren zabe, duk da cewa an fara zabe da karfe 8:00 na safe.

Google search engine

Takardar zaben ta nuna jam’iyyu guda shida kawai: APC, Boot Party, Labour Party (LP), PRP, NNPP da SDP, ba PDP da ADC ba.

Sakataren PDP na Borno, Amos Adziba, ya ce jam’iyyar ta janye daga zaben ne saboda rashin yarda da hukumar zabe da kuma tsadar kudin fom din sha’awa shiga takara da na nadin dan takara.

Shugaban Hukumar Zabe ta jihar Borno, Tahir Shettima, ya ce hukumar na aiki ne bisa doka kuma a muradin dukkan jam’iyyun da suka nuna sha’awa wajen zaben.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

NNPP ta bukaci Fadar Shugaban Nijeriya ta wanke Kwankwaso daga zargin tallafa wa ta’addanci

Jam’iyyar NNPP reshen Kano ta bukaci Fadar Shugaban Nijeriya da Ofishin Mai Ba Shugaban Ƙasa Shawara kan Tsaro (NSA) su fito su wanke jagoranta na...

Kotu a Kano ta daure jarumar Kannywood Samha Inuwa watanni 6 a gidan gyaran hali

Alkalin Babbar Kotun Tarayya da ke Kano, Mai shari’a S.M. Shuaibu, ya yanke wa jarumar Kannywood, Saadatu Mohammed Inuwa wadda aka fi sani da Samha,...

Mafi Shahara