Mataimakin Shugaban Nijeriya, Kashim Shettima, ya ce ana iya gane dan Nijeriya a ko’ina cikin duniya, ciki har da London, saboda irin izza da kwarin gwiwa da ‘yan Nijeriya ke nunawa a tafiyarsu da mu’amalarsu.
Shettima ya bayyana hakan ne a wajen bikin kammala karatun Senior Executive Course 47 a cibiyar NIPSS da ke Kuru, jihar Filato, inda ya ce ‘yan Nijeriya na tafiya da cikakken kwarin gwiwa da alfahari da asalinsu.
Hakazalika ya jaddada cewa wannan gwamnati ba za ta bari Nijeriya ta gaza ba, yana mai cewa Nijeriya ita ce ginshikin makomar bakar fata a duniya, kuma dole ne kasar ta yi aiki domin amfanin kanta da duniya baki daya.



