Kotu a kasar Bénin ta bada sammacin kama fitaccen dan gwagwarmayar kasar mai fafitikar kare hakkin Afirka Kemi Seba bisa tuhumar sa da aikata laifuka
A cikin laifukaan da ake zargin shi har da na neman tada zaune tsaye da na kiran al’ummar su yi bore da yin wa gwamnati tawaye
Wannan sammaci ya biyo bayan wani bidiyo da dan fafitikar ya wallafa a shafinsa na sada zumanta inda ya danganta sojojin da suka yi yunkurin juyin mulkin rana 7 ga watan Disemba a Bénin da ‘yan kishin kasa



