DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Ministocin kasashen ECOWAS sun yi bitar barazanar tsaro da inganta tattalin arziki a taron kungiyar

-

Taron Ministocin ECOWAS karo na 95 ya kammala a Abuja bayan kwanaki na tattaunawa kan matsalolin tsaro, siyasa da tattalin arziki a yankin Yammacin Afirka.

A taron da aka gudanar daga 10 zuwa 12 ga watan Disamba, ministocin sun tattauna barazanar ta’addanci a yankin Sahel, yaduwar makamai ba bisa ka’ida ba, laifuffukan ƙetare ƙasashe, matsalar tsaron teku a Tekun Guinea, da kuma juyin mulkin da ba bisa tsarin dimokuraɗiyya ba.

Google search engine

Da yake jawabin rufe taron, Ministan Harkokin Wajen Saliyo, Timothy Kabba, ya ce ECOWAS ta jaddada cewa dimokuraɗiyya, bin doka da oda, da tsarin mulki na gaskiya ba za su zama abin sulhu ba, yana mai cewa haɗin kai ne makamin yankin wajen shawo kan kalubalen da ke gabansa.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

El-Rufai ya zargi gwamnatin Tinubu da hannu a yunƙurin sanya Kwankwaso cikin jerin takunkumin Amurka

Tsohon gwamnan Kaduna, Malam Nasir El-Rufai, ya yi zargin cewa gwamnatin Shugaba Bola Ahmed Tinubu na iya kasancewa a bayan yunƙurin dan Majalisar Dokokin Amurka,...

Shehu Sani ya karyata El-Rufai kan batun bacewar Dadiyata

Tsohon Sanatan Kaduna ta Tsakiya, Comrade Shehu Sani, ya karyata ikirarin tsohon gwamnan Kaduna, Malam Nasir El-Rufai, cewa Abubakar Idris wanda aka fi sani da...

Mafi Shahara