DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Tsohon Sanata a Nijeriya ya bukaci shugaba Tinubu ya yi amfani da karfin soja a kan Burkina Faso domin sako sojojin Nijeriya da ke tsare a kasar

-

Tsohon ɗan majalisar dattawa daga jihar Ekiti kuma jigo a jam’iyyar APC, Sanata Ayodele Arise, ya bukaci Shugaba Tinubu da ya yi la’akari da amfani da karfin soji kan ƙasar Burkina Faso domin ganin an sako sojojin Nijeriya da ake tsare da su a can.

Arise ya bayyana hakan ne a ranar Asabar yayin wata hira da ya yi a gidan talabijin na Arise TV, inda ya ce duk da cewa sojojin Nijeriya na fuskantar manyan ƙalubale a gida sakamakon ta’addanci da ‘yan bindiga, bai kamata a kawar da zaɓin daukar matakin soja kan Burkina Faso ba.

Google search engine

Ya tuno da wani misali na tarihi, inda ya ambaci harin da Isra’ila ta kai Entebbe a Uganda a 1976, yana mai cewa irin wannan mataki na iya tilasta wa shugabannin Burkina Faso sake tunani. A cewarsa, Nijeriya na bukatar ta nuna wa makwabtanta cewa duk da kyakkyawar mu’amala, ba za a yarda a raina ƙasar ba.

Sanatan, wanda ya taba wakiltar Ekiti ta Arewa a majalisar dattawa, ya kuma bayyana goyon bayansa ga matakin soja da aka dauka kwanan nan a Jamhuriyar Benin domin dakile yunkurin juyin mulki.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

NNPP ta bukaci Fadar Shugaban Nijeriya ta wanke Kwankwaso daga zargin tallafa wa ta’addanci

Jam’iyyar NNPP reshen Kano ta bukaci Fadar Shugaban Nijeriya da Ofishin Mai Ba Shugaban Ƙasa Shawara kan Tsaro (NSA) su fito su wanke jagoranta na...

Kotu a Kano ta daure jarumar Kannywood Samha Inuwa watanni 6 a gidan gyaran hali

Alkalin Babbar Kotun Tarayya da ke Kano, Mai shari’a S.M. Shuaibu, ya yanke wa jarumar Kannywood, Saadatu Mohammed Inuwa wadda aka fi sani da Samha,...

Mafi Shahara