DCL Hausa Radio
Kaitsaye

An yi ajalin wata mace mai juna biyu da wani karamin yaro a cikin birnin Kano

-

Al’ummar Sheka Sabuwar Gandu a karamar hukumar Kano Municipal sun shiga firgici a daren Asabar bayan wasu da ba a san ko su waye ba sun yi ajalin wata mata mai juna biyu tare da danta mai watanni 18 a cikin gidansu.

Lamarin ya faru ne da misalin karfe 8 na dare, lokacin da mijin matar ya dawo daga aiki ya tarar da kofar gida a kulle, inda bayan ya shiga ya gano gawar matar da jaririn a ciki.

Google search engine

Wani jagora a unguwar, Ahmad Sani, ya ce al’umma sun kadu matuka, yana mai korafin rashin jami’an tsaro a yankin duk da an gina ofishin ‘yan sanda, tare da rokon Kwamishinan ‘yan sandan Kano, Dr Ibrahim Adamu Bakori, da ya dauki matakin gaggawa.

‘Yan sanda sun ce bincike na gudana, yayin da mazauna yankin ke neman a hanzarta kamo wadanda suka aikata laifin.

1 COMMENT

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Har yanzu bamu kammala bincike ba shiyasa bamu gurfanar da El-rufa’i a gaban kotu ba – EFCC

Hukumar EFCC, mai yaki a cin hanci da rashawa a Nijeriya ta bayyana dalilin da ya sa har yanzu ba ta kai tsohon gwamnan Kaduna,...

Wanene sabon Shugaban Rundunar ‘Yan Sandan Nijeriya, Olatunji Disu?

AIG Olatunji Disu ya kasance gogaggen jami’i wanda aka nada don jagorantar rundunar 'yan sandan kasar a matsayin IGP na 23. A cewar fadar shugaban...

Mafi Shahara