Al’ummar Sheka Sabuwar Gandu a karamar hukumar Kano Municipal sun shiga firgici a daren Asabar bayan wasu da ba a san ko su waye ba sun yi ajalin wata mata mai juna biyu tare da danta mai watanni 18 a cikin gidansu.
Lamarin ya faru ne da misalin karfe 8 na dare, lokacin da mijin matar ya dawo daga aiki ya tarar da kofar gida a kulle, inda bayan ya shiga ya gano gawar matar da jaririn a ciki.
Wani jagora a unguwar, Ahmad Sani, ya ce al’umma sun kadu matuka, yana mai korafin rashin jami’an tsaro a yankin duk da an gina ofishin ‘yan sanda, tare da rokon Kwamishinan ‘yan sandan Kano, Dr Ibrahim Adamu Bakori, da ya dauki matakin gaggawa.
‘Yan sanda sun ce bincike na gudana, yayin da mazauna yankin ke neman a hanzarta kamo wadanda suka aikata laifin.




Allah ya shiga tsakanin nagari da mugu allah ya jikan mamatan