DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Ba zan koma APC ba, duk kuwa da bibiyata da fadar shugaban kasa ke yi – Sanata Natasha

-

Sanatar Kogi ta Tsakiya, Natasha Akpoti-Uduaghan, ta ce ba ta da niyyar ficewa daga jam’iyyar PDP zuwa APC, duk da cewa ana ta yi mata tayin sauya sheka daga wasu mutane da ke da alaka da fadar shugaban kasa da kuma wasu ’yan majalisa.

Ta bayyana hakan ne a wata hira da ta yi a shirin Mic On Podcast, inda ta ce ko da rikicin da ke addabar PDP ya tsananta, ba za ta bi sahun masu sauya jam’iyya ba, tana mai cewa ba ta yarda da barazana ko rarrashi na siyasa.

Google search engine

Sanatar ta kara da cewa an sha tuntubarta a lokuta daban-daban, har da kwanan nan, amma ta fi son ci-gaba da zama a PDP, tana mai cewa har yanzu tana tattaunawa kan makomarta ta siyasa, ciki har da yiwuwar sake tsayawa takara, amma ba a yanke hukunci ba tukuna.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Dan majalisar wakilan Nijeriya ya sauys sheka daga PDP zuwa ADC

Dan majalisar tarayya mai wakiltar mazabar Tambuwal/Kebbe a jihar Sokoto, Abdussamad Dasuki ya sanar da ficewarsa daga jam’iyyar PDP, inda ya koma ADC. A cikin wasiƙar...

Sanata Wamako ya raba wa marayu su 10,000 tallafin N1,000 kowane a jihar Sokoto

Tsohon gwamnan jihar Sokoto kuma Sanata mai wakiltar Sokoto ta Arewa, Aliyu Magatakarda Wamakko, ya bayar da tallafin miliyan 10, ga mutane dubu 10 da...

Mafi Shahara