Sanatar Kogi ta Tsakiya, Natasha Akpoti-Uduaghan, ta ce ba ta da niyyar ficewa daga jam’iyyar PDP zuwa APC, duk da cewa ana ta yi mata tayin sauya sheka daga wasu mutane da ke da alaka da fadar shugaban kasa da kuma wasu ’yan majalisa.
Ta bayyana hakan ne a wata hira da ta yi a shirin Mic On Podcast, inda ta ce ko da rikicin da ke addabar PDP ya tsananta, ba za ta bi sahun masu sauya jam’iyya ba, tana mai cewa ba ta yarda da barazana ko rarrashi na siyasa.
Sanatar ta kara da cewa an sha tuntubarta a lokuta daban-daban, har da kwanan nan, amma ta fi son ci-gaba da zama a PDP, tana mai cewa har yanzu tana tattaunawa kan makomarta ta siyasa, ciki har da yiwuwar sake tsayawa takara, amma ba a yanke hukunci ba tukuna.



