DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Jam’iyyar ADC ta fara rajista da tantance mambobi na kwanaki 90 a fadin Nijeriya

-

Jam’iyyar African Democratic Congress (ADC) ta fara shirin rajista, tantancewa da kuma jawo sabbin mambobi na tsawon kwanaki 90 a fadin Nijeriya, domin karfafa jam’iyyar daga tushe.

Jam’iyyar ta bayyana hakan ne a cikin wata sanarwa da sakataren yada labaranta na kasa, Malam Bolaji Abdullahi, ya fitar a ranar Asabar, inda ya ce an dauki matakin ne bayan kammala taron kwamitin gudanarwa na kasa da aka gudanar a ranar 27 ga watan Nuwamba, 2025, bisa tanadin kundin tsarin jam’iyyar.

Google search engine

ADC ta kuma sanar da shirinta na gudanar da tarukan zabe a matakin rumfunan zabe, mazabu da kananan hukumomi daga ranar 20 zuwa 27 ga Janairu, 2026, kafin babban taron kasa da aka shirya gudanarwa a watan Fabrairu, 2026 a Abuja.

Jam’iyyar ta ce wannan shiri na da matukar muhimmanci wajen karfafa hadin kan mambobi da tsari a fadin kasa.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Rashin tabbas da matsalolin tsaro na barazana ga burin ECOWAS na 2050 – Shugaban ECOWAS, Touray

Shugaban kungiyar ECOWAS, Omar Touray, ya ce rashin tabbas a duniya, matsalolin tsaro da matsin tattalin arziki na hana kungiyar cimma burinta na Vision 2050,...

An yi ajalin wata mace mai juna biyu da wani karamin yaro a cikin birnin Kano

Al’ummar Sheka Sabuwar Gandu a karamar hukumar Kano Municipal sun shiga firgici a daren Asabar bayan wasu da ba a san ko su waye ba...

Mafi Shahara