DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Kungiyar dattawan Arewacin Nijeriya ta bukaci a gaggauta janye yarjejeniyar hukumar haraji ta Nijeriya da kasar Faransa

-

Kungiyar dattawan Arewa ta bukaci gwamnatin Nijeriya da ta gaggauta soke yarjejeniyar fahimta da Hukumar Tara Haraji ta Nijeriya (FIRS) ta kulla da hukumar haraji ta Faransa,, tana mai cewa yarjejeniyar na barazana ga ikon tattalin arziki da tsaron kasa.

A wata budaddiyar wasika da ta aikewa gwamnatin Nijeriya, majalisar dattawa da majalisar wakilai, kungiyar ta bayyana yarjejeniyar a matsayin “hadari ga bayanan haraji,” wadda za ta iya bai wa wata kasa ikon mallakar muhimman bayanan tattalin arzikin Nijeriya.

Google search engine

Wasikar wadda mai magana da yawun kungiyar, Farfesa Abubakar Jiddere ya sanya wa hannu, ta ce yarjejeniyar ta wuce hadin gwiwar fasaha kawai, tana mai gargadin cewa tana zama wata hanya kai tsaye da ba ta da kariya zuwa cibiyar tsarin haraji na Nijeriya, tare da mika bayanai masu matukar muhimmanci ga ikon wata kasa ta waje.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Rashin tabbas da matsalolin tsaro na barazana ga burin ECOWAS na 2050 – Shugaban ECOWAS, Touray

Shugaban kungiyar ECOWAS, Omar Touray, ya ce rashin tabbas a duniya, matsalolin tsaro da matsin tattalin arziki na hana kungiyar cimma burinta na Vision 2050,...

An yi ajalin wata mace mai juna biyu da wani karamin yaro a cikin birnin Kano

Al’ummar Sheka Sabuwar Gandu a karamar hukumar Kano Municipal sun shiga firgici a daren Asabar bayan wasu da ba a san ko su waye ba...

Mafi Shahara