DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Rashin tabbas da matsalolin tsaro na barazana ga burin ECOWAS na 2050 – Shugaban ECOWAS, Touray

-

Shugaban kungiyar ECOWAS, Omar Touray, ya ce rashin tabbas a duniya, matsalolin tsaro da matsin tattalin arziki na hana kungiyar cimma burinta na Vision 2050, yana mai cewa ta’addanci a Sahel da raunin hadin kan kasa da kasa na kawo cikas ga ci-gaban yankin.

Touray ya bayyana haka ne a taron shugabannin ECOWAS karo na 69 an Abuja, inda ya ce wadannan kalubale na tilasta wa kasashen yankin daukar matakai masu wahala da ka iya shafar dunkulewar kungiyar.

Google search engine

Touray ya kara da cewa duk da matsalolin tsaro da siyasa da ke karkatar da hankali daga ci-gaba, ECOWAS za ta ci gaba da mayar da hankali kan hadewar tattalin arziki domin cimma burin Vision 2050.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Dan majalisar wakilan Nijeriya ya sauys sheka daga PDP zuwa ADC

Dan majalisar tarayya mai wakiltar mazabar Tambuwal/Kebbe a jihar Sokoto, Abdussamad Dasuki ya sanar da ficewarsa daga jam’iyyar PDP, inda ya koma ADC. A cikin wasiƙar...

Sanata Wamako ya raba wa marayu su 10,000 tallafin N1,000 kowane a jihar Sokoto

Tsohon gwamnan jihar Sokoto kuma Sanata mai wakiltar Sokoto ta Arewa, Aliyu Magatakarda Wamakko, ya bayar da tallafin miliyan 10, ga mutane dubu 10 da...

Mafi Shahara