Shugaban kungiyar ECOWAS, Omar Touray, ya ce rashin tabbas a duniya, matsalolin tsaro da matsin tattalin arziki na hana kungiyar cimma burinta na Vision 2050, yana mai cewa ta’addanci a Sahel da raunin hadin kan kasa da kasa na kawo cikas ga ci-gaban yankin.
Touray ya bayyana haka ne a taron shugabannin ECOWAS karo na 69 an Abuja, inda ya ce wadannan kalubale na tilasta wa kasashen yankin daukar matakai masu wahala da ka iya shafar dunkulewar kungiyar.
Touray ya kara da cewa duk da matsalolin tsaro da siyasa da ke karkatar da hankali daga ci-gaba, ECOWAS za ta ci gaba da mayar da hankali kan hadewar tattalin arziki domin cimma burin Vision 2050.



