DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Dangote ya zayyana irin zagon kasan da ake yi wa matatun mai a Nijeriya

-

Shugaban matatar man Dangote, Aliko Dangote, ya ce kungiyoyin da ke zagon kasa a bangaren mai da gas a Najeriya da ya kira “oil mafia” sun fi karfin masu safarar kwayoyi.

Ya bayyana cewa an saci kayan matatar Dangote da darajarsu ta kai $82m, lamarin da ya janyo karin tsaro a matatar.

Google search engine

Dangote ya ce an yi gagarumin zagon kasa, har da cire muhimmin sashi daga babbar injin tukunyar ruwa yayin aiki, da kuma lalata bututun man fetur a fadin kasa. Ya ce wadannan ayyuka na nufin kassara aikin tace mai a cikin gida domin ci gaba da dogaro da shigo da fetur.

Jaridar Punch ta ruwaito shi na jaddada cewa zagon kasar da ake yi wa matatun mai na cikin gida na barazana ga tattalin arzikin kasa.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Nijeriya ta musanta zargin leken asiri kan jirginta da ke Burkina-Faso

Rundunar Sojin Sama ta Najeriya ta musanta zargin leken asiri da ake jinginawa jirginta a Burkina-Faso Rundunar Sojin Sama ta Najeriya (NAF) ta karyata jita-jitar da...

Tsadar kudin haya na hana samari aure a Sokoto – Daily Trust

Mazauna Jihar Sokoto sun koka kan tashin kudin haya, suna cewa lamarin na jinkirta aure tare da jefa matasa cikin matsin tattalin arziki da barazanar...

Mafi Shahara