Shugaban Kamfanin Dangote, Aliko Dangote, ya shigar da ƙorafi ga Hukumar ICPC yana zargin Shugaban Hukumar NMDPRA, Farouk Ahmed, da cin hanci da almundahanar kudade.
A ƙorafin da ya miƙa ta hannun lauyansa, Dangote ya buƙaci a kama, bincika tare da gurfanar da Farouk bisa zargin kashe fiye da dala miliyan bakwai wajen karatun ‘ya’yansa a Switzerland, ba tare da sahihin tushen kuɗi ba.
Jaridar Punch ta ruwaito Dangote ya ce Farouk ya yi amfani da mukaminsa wajen karkatar da kuɗaɗen gwamnati don amfanin kansa, lamarin da ke saɓa wa dokar rikon amana ga jami’an gwamnati.
Inda ya bukaci ICPC ta ɗauki mataki cikin gaggawa domin kare gaskiya da martabar gwamnati a kasar.



