DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Jerin attajiran Afirka guda 22 a shekarar 2025 -Forbes

-

Attajirin Najeriya, Aliko Dangote, ya sake rike matsayi na daya karo na 14 a jere da dukiyar dala biliyan 23.9, sakamakon fara aiki da matatar man fetur dinsa da ke Lagos.

Mujallar Forbes da ta saba bincike da wallafa sunayen attajirai a duniya ta bayyana cewa attajiran Afirka sun kai 22 a shekarar 2025, inda jimillar dukiyarsu ta haura dala biliyan 105, karo na farko a tarihin nahiyar.

Google search engine

Duk da kalubalen tattalin arziki, kasuwannin hannun jari na duniya sun taimaka wajen karuwar dukiyar masu arziki a Afirka.

Rahoton ya ambato kasashen Afirka ta Kudu ne ke da mafi yawan attajirai (7), sai Najeriya da Masar da ke da 4 kowannensu, yayin da Moroko ke da 3.

Ga jerin attajiran Afirka a 2025:

Aliko Dangote – $23.9bn (Najeriya)

Johann Rupert & iyali – $14bn (Afirka ta Kudu)

Nicky Oppenheimer & iyali – $10.4bn (Afirka ta Kudu)

Nassef Sawiris – $9.6bn (Masar)

Mike Adenuga – $6.8bn (Najeriya)

Abdulsamad Rabiu – $5.1bn (Najeriya)

Naguib Sawiris – $5bn (Masar)

Koos Bekker – $3.4bn (Afirka ta Kudu)

Mohamed Mansour – $3.4bn (Masar)

Patrice Motsepe – $3bn (Afirka ta Kudu)

Issad Rebrab & iyali – $3bn (Aljeriya)

Mohammed Dewji – $2.2bn (Tanzaniya)

Michiel Le Roux – $2.2bn (Afirka ta Kudu)

Othman Benjelloun & iyali – $1.6bn (Moroko)

Anas Sefrioui & iyali – $1.6bn (Moroko)

Aziz Akhannouch & iyali – $1.5bn (Moroko)

Jannie Mouton & iyali – $1.5bn (Afirka ta Kudu)

Femi Otedola – $1.5bn (Najeriya)

Christoffel Wiese – $1.5bn (Afirka ta Kudu)

Youssef Mansour – $1.4bn (Masar)

Yasseen Mansour – $1.2bn (Masar)

Strive Masiyiwa – $1.2bn (Zimbabwe)

Rahoton na Forbes ya nuna cewa duk da matsin tattalin arziki da kalubalen siyasa a sassan Afirka, manyan ’yan kasuwa sun ci gaba da bunkasa dukiyarsu, lamarin da ke kara haskaka rawar da kasuwanci da zuba jari ke takawa wajen ci gaban nahiyar.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Har yanzu bamu kammala bincike ba shiyasa bamu gurfanar da El-rufa’i a gaban kotu ba – EFCC

Hukumar EFCC, mai yaki a cin hanci da rashawa a Nijeriya ta bayyana dalilin da ya sa har yanzu ba ta kai tsohon gwamnan Kaduna,...

Wanene sabon Shugaban Rundunar ‘Yan Sandan Nijeriya, Olatunji Disu?

AIG Olatunji Disu ya kasance gogaggen jami’i wanda aka nada don jagorantar rundunar 'yan sandan kasar a matsayin IGP na 23. A cewar fadar shugaban...

Mafi Shahara