Attajirin Najeriya, Aliko Dangote, ya sake rike matsayi na daya karo na 14 a jere da dukiyar dala biliyan 23.9, sakamakon fara aiki da matatar man fetur dinsa da ke Lagos.
Mujallar Forbes da ta saba bincike da wallafa sunayen attajirai a duniya ta bayyana cewa attajiran Afirka sun kai 22 a shekarar 2025, inda jimillar dukiyarsu ta haura dala biliyan 105, karo na farko a tarihin nahiyar.
Duk da kalubalen tattalin arziki, kasuwannin hannun jari na duniya sun taimaka wajen karuwar dukiyar masu arziki a Afirka.
Rahoton ya ambato kasashen Afirka ta Kudu ne ke da mafi yawan attajirai (7), sai Najeriya da Masar da ke da 4 kowannensu, yayin da Moroko ke da 3.
Ga jerin attajiran Afirka a 2025:
Aliko Dangote – $23.9bn (Najeriya)
Johann Rupert & iyali – $14bn (Afirka ta Kudu)
Nicky Oppenheimer & iyali – $10.4bn (Afirka ta Kudu)
Nassef Sawiris – $9.6bn (Masar)
Mike Adenuga – $6.8bn (Najeriya)
Abdulsamad Rabiu – $5.1bn (Najeriya)
Naguib Sawiris – $5bn (Masar)
Koos Bekker – $3.4bn (Afirka ta Kudu)
Mohamed Mansour – $3.4bn (Masar)
Patrice Motsepe – $3bn (Afirka ta Kudu)
Issad Rebrab & iyali – $3bn (Aljeriya)
Mohammed Dewji – $2.2bn (Tanzaniya)
Michiel Le Roux – $2.2bn (Afirka ta Kudu)
Othman Benjelloun & iyali – $1.6bn (Moroko)
Anas Sefrioui & iyali – $1.6bn (Moroko)
Aziz Akhannouch & iyali – $1.5bn (Moroko)
Jannie Mouton & iyali – $1.5bn (Afirka ta Kudu)
Femi Otedola – $1.5bn (Najeriya)
Christoffel Wiese – $1.5bn (Afirka ta Kudu)
Youssef Mansour – $1.4bn (Masar)
Yasseen Mansour – $1.2bn (Masar)
Strive Masiyiwa – $1.2bn (Zimbabwe)
Rahoton na Forbes ya nuna cewa duk da matsin tattalin arziki da kalubalen siyasa a sassan Afirka, manyan ’yan kasuwa sun ci gaba da bunkasa dukiyarsu, lamarin da ke kara haskaka rawar da kasuwanci da zuba jari ke takawa wajen ci gaban nahiyar.



