Shugaban Nijeriya, Bola Ahmed Tinubu, ya bukaci Rundunar Sojojin Ƙasa ta Nijeriya da ta kiyaye rashin shiga harkokin siyasa tare da bin kundin tsarin mulki.
Ya bayyana hakan ne a wajen bude taron shekara-shekara na Shugaban Sojojin Ƙasa da ke gudana a Legas, inda Mataimakin Shugaban Ƙasa, Kashim Shettima, ya wakilce shi.
Jaridar Daily Trust ta ce Tinubu ya jaddada cewa aikin sojoji shi ne kare ƙasa da ’yan ƙasa, yana mai tabbatar da cewa gwamnatinsa za ta ci gaba da tallafa wa rundunar ta fuskar kayan aiki da horo.
Ya yaba da nasarorin da sojoji ke samu a yaki da ta’addanci, yayin da Gwamnan Lagos, Babajide Sanwo-Olu, da Ministan Tsaro, Janar Christopher Musa, suka jaddada muhimmancin tsaro da haɗin gwiwar hukumomi wajen kare kasa.



