DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Tinubu ya bukaci sojoji su ci gaba da zama ‘yan ba ruwan mu a siyasa

-

Shugaban Nijeriya, Bola Ahmed Tinubu, ya bukaci Rundunar Sojojin Ƙasa ta Nijeriya da ta kiyaye rashin shiga harkokin siyasa tare da bin kundin tsarin mulki.

Ya bayyana hakan ne a wajen bude taron shekara-shekara na Shugaban Sojojin Ƙasa da ke gudana a Legas, inda Mataimakin Shugaban Ƙasa, Kashim Shettima, ya wakilce shi.

Google search engine

Jaridar Daily Trust ta ce Tinubu ya jaddada cewa aikin sojoji shi ne kare ƙasa da ’yan ƙasa, yana mai tabbatar da cewa gwamnatinsa za ta ci gaba da tallafa wa rundunar ta fuskar kayan aiki da horo.

Ya yaba da nasarorin da sojoji ke samu a yaki da ta’addanci, yayin da Gwamnan Lagos, Babajide Sanwo-Olu, da Ministan Tsaro, Janar Christopher Musa, suka jaddada muhimmancin tsaro da haɗin gwiwar hukumomi wajen kare kasa.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Har yanzu bamu kammala bincike ba shiyasa bamu gurfanar da El-rufa’i a gaban kotu ba – EFCC

Hukumar EFCC, mai yaki a cin hanci da rashawa a Nijeriya ta bayyana dalilin da ya sa har yanzu ba ta kai tsohon gwamnan Kaduna,...

Wanene sabon Shugaban Rundunar ‘Yan Sandan Nijeriya, Olatunji Disu?

AIG Olatunji Disu ya kasance gogaggen jami’i wanda aka nada don jagorantar rundunar 'yan sandan kasar a matsayin IGP na 23. A cewar fadar shugaban...

Mafi Shahara