DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Kotu a Kano ta tura matar da ta yi ajalin diyar kishiyarta shekaru 10 a gidan yari

-

Babbar Kotun Jihar Kano da ke zama a Kano Municipal ta yankewa wata mace mai suna Hafsa Umar hukuncin daurin shekara 10 a gidan gyaran hali bayan ta same ta da laifin ajalin ’yar mijinta.

Kotun ta saurari cewa Hafsa ta yi wa yarinyar duka ne bayan zargin ta da satar kuli-kuli, inda masu gabatar da ƙara suka bayyana cewa dukan ya wuce kima har ya jawo mutuwar yarinyar.

Google search engine

Rahoton jaridar Daily Trust ya ce a yayin shari’ar, lauyar gwamnati Barrista Hafsa Adam da Barrista Jamilu Abubakar sun gabatar da shaidu da hujjoji domin tabbatar da laifin wadda ake tuhuma, yayin da bangaren kariya ya gabatar da shaidu biyu.

Da take yanke hukunci, Mai shari’a Aisha Mahmud ta ce ɓangaren ƙara ya tabbatar da laifin wanda ake tuhuma ba tare da shakka ba.

Alkalin kotun ta bayyana cewa laifin ya saba wa Sashe na 226 na Kundin Hukunta Laifuka (Penal Code), tare da yanke mata hukuncin shekara 10 a gidan gyaran hali.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Babu adawa a jihar Plateau a zaben 2027 – Caleb Muftwang

Gwamnan Jihar Plateau, Caleb Manasseh Mutfwang, ya bayyana cewa zuwa zaben 2027 jam’iyyarsa ba za ta samu adawa a jihar ba. Ya fadi hakan ne...

Obasanjo ya musanta rubuta sanarwar mutuwarsa

Tsohon Shugaban Nijeriya, Olusegun Obasanjo, ya musanta wani rubutu da ke yawo a kafafen sada zumunta da ke ikirarin cewa ya fitar da sanarwar mutuwarsa. Rubutun...

Mafi Shahara