DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Tinubu da Ministan Kudin Nijeriya sun yi baki biyu kan kudin shigar 2025

-

Ministan Kuɗi kuma na Nijeriya, Wale Edun, ya saɓa wa furucin Shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu, inda ya ce gwamnatin tarayya ba ta kai burin kudaden shiga na 2025 ba.

Edun ya bayyana cewa zuwa yanzu gwamnati ta samu naira tiriliyan 10.7, ne kacal daga cikin naira tiriliyan 40.8 da aka yi hasashen samu a shekarar 2025.

Google search engine

Tun da farko, Tinubu ya shaida wa jama’a cewa Najeriya ta kai burin kudaden shiga na 2025 tun watan Agusta, tare da jaddada cewa gwamnati ba za ta ƙara dogaro da rancen kuɗi wajen aiwatar da kasafin kuɗi ba.

Sai dai bayanin Edun ya nuna cewa akwai gagarumin gibi a kudaden shiga na bana, lamarin da ke sake tayar da hankula kan ɗorewar harkokin kuɗin gwamnatin Najeriya.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

FIFA ta sanya $60 a matsayin kudin tikitin kallon kofin duniya na 2026

Hukumar kwallon kafa ta duniya FIFA ta ƙaddamar da sabon rukuni na tikiti a dalar Amurka 60 ga kowane ɗayan wasannin 104 na Gasar Kofin...

Likitoci sun tsunduma yajin aiki a Ingila

Ƙungiyar British Medical Association (BMA) ta tabbatar da ci gaba da gudanar da yajin aiki, bayan kashi 83 cikin ɗari na mambobinta sun amince da...

Mafi Shahara