DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Tinubu da Ministan Kudin Nijeriya sun yi baki biyu kan kudin shigar 2025

-

Ministan Kuɗi kuma na Nijeriya, Wale Edun, ya saɓa wa furucin Shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu, inda ya ce gwamnatin tarayya ba ta kai burin kudaden shiga na 2025 ba.

Edun ya bayyana cewa zuwa yanzu gwamnati ta samu naira tiriliyan 10.7, ne kacal daga cikin naira tiriliyan 40.8 da aka yi hasashen samu a shekarar 2025.

Google search engine

Tun da farko, Tinubu ya shaida wa jama’a cewa Najeriya ta kai burin kudaden shiga na 2025 tun watan Agusta, tare da jaddada cewa gwamnati ba za ta ƙara dogaro da rancen kuɗi wajen aiwatar da kasafin kuɗi ba.

Sai dai bayanin Edun ya nuna cewa akwai gagarumin gibi a kudaden shiga na bana, lamarin da ke sake tayar da hankula kan ɗorewar harkokin kuɗin gwamnatin Najeriya.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Babu adawa a jihar Plateau a zaben 2027 – Caleb Muftwang

Gwamnan Jihar Plateau, Caleb Manasseh Mutfwang, ya bayyana cewa zuwa zaben 2027 jam’iyyarsa ba za ta samu adawa a jihar ba. Ya fadi hakan ne...

Obasanjo ya musanta rubuta sanarwar mutuwarsa

Tsohon Shugaban Nijeriya, Olusegun Obasanjo, ya musanta wani rubutu da ke yawo a kafafen sada zumunta da ke ikirarin cewa ya fitar da sanarwar mutuwarsa. Rubutun...

Mafi Shahara