Shugaban Amurka Donald Trump ya faɗaɗa haramcin shiga Amurka, inda aka hana karin ‘yan ƙasashe biyar.
Fadar White House ta ce an ɗauki wannan mataki ne don kare tsaron Amurka, kuma dokar za ta fara aiki daga ranar 1 ga Janairu.
Cikakken haramcin shiga ƙasar zai shafi ‘yan Burkina Faso, Mali, Nijar, Sudan ta Kudu da Syria.


