Mai ba Shugaban Majalisar Dattawa shawara kan sadarwa, Kenny Okolugbo, ya musanta rahotannin da ke yawo a kafafen sada zumunta da ke cewa Shugaban Majalisar, Godswill Akpabio, ba shi da lafiya.
Okolugbo ya bayyana haka ne a wata hira da ya yi a shirin Morning Brief na Channels TV, inda ya ce Akpabio lafiyarsa kalau kuma yana ci-gaba da gudanar da ayyukansa na yau da kullum a majalisa.
Ya kwatanta jita-jitar da irin wadda aka taba yadawa kan Ministan Babban Birnin Tarayya, Nyesom Wike, inda aka ce ba shi da lafiya amma washegari aka gan shi yana kaddamar da ayyuka a bainar jama’a.
Okolugbo ya bukaci a sanya tsari mai tsauri kan kafafen sada zumunta domin dakile yada labaran karya, yana mai cewa doka ta hana yada bayanan da ba a tantance sahihancinsu ba.



