DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Akpabio yana nan garas cikin koshin lafiya – Hadiminsa

-

Mai ba Shugaban Majalisar Dattawa shawara kan sadarwa, Kenny Okolugbo, ya musanta rahotannin da ke yawo a kafafen sada zumunta da ke cewa Shugaban Majalisar, Godswill Akpabio, ba shi da lafiya.

Okolugbo ya bayyana haka ne a wata hira da ya yi a shirin Morning Brief na Channels TV, inda ya ce Akpabio lafiyarsa kalau kuma yana ci-gaba da gudanar da ayyukansa na yau da kullum a majalisa.

Google search engine

Ya kwatanta jita-jitar da irin wadda aka taba yadawa kan Ministan Babban Birnin Tarayya, Nyesom Wike, inda aka ce ba shi da lafiya amma washegari aka gan shi yana kaddamar da ayyuka a bainar jama’a.

Okolugbo ya bukaci a sanya tsari mai tsauri kan kafafen sada zumunta domin dakile yada labaran karya, yana mai cewa doka ta hana yada bayanan da ba a tantance sahihancinsu ba.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Babu adawa a jihar Plateau a zaben 2027 – Caleb Muftwang

Gwamnan Jihar Plateau, Caleb Manasseh Mutfwang, ya bayyana cewa zuwa zaben 2027 jam’iyyarsa ba za ta samu adawa a jihar ba. Ya fadi hakan ne...

Obasanjo ya musanta rubuta sanarwar mutuwarsa

Tsohon Shugaban Nijeriya, Olusegun Obasanjo, ya musanta wani rubutu da ke yawo a kafafen sada zumunta da ke ikirarin cewa ya fitar da sanarwar mutuwarsa. Rubutun...

Mafi Shahara