DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Kotu ta amince ta bai wa Ngige beli tare da sharaɗin nemo babban jami’in gwamnati da zai tsaya masa

-

Babbar Kotun Abuja da ke Gwarinpa, ta amince tsohon Ministan Kwadago, Chris Ngige, ya cigaba da cin gajiyar belin da hukumar EFCC ta ba shi tun da farko.

Alkaliyar kotun, Mai shari’a Maryam Hassan, ta bayar da wannan hukunci ne yayin yanke shawara kan bukatar beli da lauyan Ngige, Barista Patrick Ikwueto (SAN), ya shigar a madadinsa.

Google search engine

Kotun ta umarci Ngige da ya gabatar da mai tsaya masa wanda dole ne ya kasance darakta a aikin Gwamnatin Tarayya kuma mai fili. Haka kuma, kotun ta ce dole ne mai tsayawar ya ajiye takardun filin da kuma takardun tafiyarsa a gaban kotu har sai Ngige ya karbo fasfonsa na kasa da kasa.

Tun da farko, EFCC ta ba Ngige beli ne bisa amincewar kansa, inda ta umarce shi da ya mika takardun tafiyarsa tare da gabatar da mai tsaya masa guda daya.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Babu adawa a jihar Plateau a zaben 2027 – Caleb Muftwang

Gwamnan Jihar Plateau, Caleb Manasseh Mutfwang, ya bayyana cewa zuwa zaben 2027 jam’iyyarsa ba za ta samu adawa a jihar ba. Ya fadi hakan ne...

Obasanjo ya musanta rubuta sanarwar mutuwarsa

Tsohon Shugaban Nijeriya, Olusegun Obasanjo, ya musanta wani rubutu da ke yawo a kafafen sada zumunta da ke ikirarin cewa ya fitar da sanarwar mutuwarsa. Rubutun...

Mafi Shahara