DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Kungiyar tarayyar Turai za ta karfafa hadin guiwar tsaro da Nijeriya

-

Kungiyar tarayyar Turai (EU) da Nijeriya na ɗaukar sabbin matakai domin ƙarfafa dangantakarsu ta tsaro, a wani yunƙuri na fuskantar kalubalen tsaro da ke ƙara rikitarwa a ƙasar.

Jakadan EU a Nijeriya da ECOWAS, Gautier Mignot, ya bayyana haka ne a Abuja yayin ziyarar girmamawa da ya kai wa Babban Hafsan Tsaro, Janar Olufemi Oluyede, inda ya taya shi murna kan sabon muƙaminsa.

Google search engine

Mignot ya jaddada muhimmancin Nijeriya ga EU, yana mai cewa ƙasashe 19 daga cikin 27 na EU na da ofisoshin jakadanci a Nijeriya, tare da tabbatar da ci-gaba da tallafin EU wajen magance matsalolin tsaro.

Ya ƙara da cewa tallafin EU ba na soji kaɗai ba ne, har da shirye-shiryen zaman lafiya, hana rikici, inganta shugabanci da bunƙasa hukumomi, musamman a wannan lokaci mai sarkakiya ga Nijeriya.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Babu adawa a jihar Plateau a zaben 2027 – Caleb Muftwang

Gwamnan Jihar Plateau, Caleb Manasseh Mutfwang, ya bayyana cewa zuwa zaben 2027 jam’iyyarsa ba za ta samu adawa a jihar ba. Ya fadi hakan ne...

Obasanjo ya musanta rubuta sanarwar mutuwarsa

Tsohon Shugaban Nijeriya, Olusegun Obasanjo, ya musanta wani rubutu da ke yawo a kafafen sada zumunta da ke ikirarin cewa ya fitar da sanarwar mutuwarsa. Rubutun...

Mafi Shahara