DCL Hausa Radio
Kaitsaye

INEC ta shiga tsakani kan rikicin shugabanci a PDP

-

Hukumar Zabe Mai Zaman Kanta ta Nijeriya (INEC) ta shiga tsakani kan rikicin shugabancin PDP, inda ta gayyaci bangarorin jam’iyyar biyu zuwa hedikwatarta da ke Abuja a ranar Juma’a.

 

Google search engine

Taron ya hada bangaren da Tanimu Turaki ke jagoranta da kuma bangaren Abdulrahman Mohammed, wanda ke samun goyon bayan Ministan Babban Birnin Tarayya, Nyesom Wike.

 

Da yake jawabi a wajen taron, shugaban hukumar INEC Farfesa Joash Amupitan ya ce kiran bangarorin biyu ya zama wajibi ne sakamakon ta’azzarar rikicin cikin gida a jam’iyyar ta PDP.

 

Bayan gabatar da jawabi an shiga taron sirri, inda ake sa ran samun sasanci tsakanin bangarorin da ke rikici da juna bayan haka, kamar yadda jaridar Punch ta ruwaito.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

APC ta yi wa Gwamnan jihar Plateau maraba da shiga cikinta

Jam'iyyar APC reshen jihar Plateau ta bayyana yi wa Gwamnan jihar Caleb Mutfwang maraba da shiga cikinta, bayan ficewa daga jam‘iyyar PDP.   Sakataren jam'iyyar Shitu Bamaiyi...

Tinubu ya jaddada wa Amurka kudurin kafa ‘yansandan jihohi a Nijeriya

Shugaban Nijeriya Bola Ahmed Tinubu ya sake jaddada kudurinsa na kafa 'yansandan jihohi a Nijeriya, yana mai cewa ya shaida hakan ga Amurka da sauran...

Mafi Shahara