DCL Hausa Radio
Kaitsaye

INEC ta shiga tsakani kan rikicin shugabanci a PDP

-

Hukumar Zabe Mai Zaman Kanta ta Nijeriya (INEC) ta shiga tsakani kan rikicin shugabancin PDP, inda ta gayyaci bangarorin jam’iyyar biyu zuwa hedikwatarta da ke Abuja a ranar Juma’a.

 

Google search engine

Taron ya hada bangaren da Tanimu Turaki ke jagoranta da kuma bangaren Abdulrahman Mohammed, wanda ke samun goyon bayan Ministan Babban Birnin Tarayya, Nyesom Wike.

 

Da yake jawabi a wajen taron, shugaban hukumar INEC Farfesa Joash Amupitan ya ce kiran bangarorin biyu ya zama wajibi ne sakamakon ta’azzarar rikicin cikin gida a jam’iyyar ta PDP.

 

Bayan gabatar da jawabi an shiga taron sirri, inda ake sa ran samun sasanci tsakanin bangarorin da ke rikici da juna bayan haka, kamar yadda jaridar Punch ta ruwaito.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Dan majalisar wakilan Nijeriya ya sauys sheka daga PDP zuwa ADC

Dan majalisar tarayya mai wakiltar mazabar Tambuwal/Kebbe a jihar Sokoto, Abdussamad Dasuki ya sanar da ficewarsa daga jam’iyyar PDP, inda ya koma ADC. A cikin wasiƙar...

Sanata Wamako ya raba wa marayu su 10,000 tallafin N1,000 kowane a jihar Sokoto

Tsohon gwamnan jihar Sokoto kuma Sanata mai wakiltar Sokoto ta Arewa, Aliyu Magatakarda Wamakko, ya bayar da tallafin miliyan 10, ga mutane dubu 10 da...

Mafi Shahara