DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Sojojin Nijeriya sun dakile harin ‘yan bindiga a jihar Borno

-

Rundunar sojin Nijeriya karkashin shirin ‘Operation Hadin Kai’ ta samu nasarar dakile wani hari da ‘yan ta’adda suka shirya kaddamarwa a yankin Bitta daga tsaunukan Mandara a jihar Borno.

 

Google search engine

Yayin gumurzun dai sojojin sun hallaka ‘yan ta’adda da dama kamar yadda jaridar Punch ta ruwaito.

 

Wata sanarwa da rundunar sojin ta fitar ta hannun Laftanar Kanal Sani Uba a shafinta na X, ta ce lamarin ya faru ne da misalin karfe 12 na daren Alhamis, inda sojojin suka gano motsin ‘yan ta’addan zuwa yankin.

 

Bayan fatattakar su, sanarwar ta kuma ce an samu nasarar kwato tarin makamai da sauran kayayyakin da ‘yan bindigar ke amfani da su wajen kaddamar da hare-hare kan al’umma.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

APC ta yi wa Gwamnan jihar Plateau maraba da shiga cikinta

Jam'iyyar APC reshen jihar Plateau ta bayyana yi wa Gwamnan jihar Caleb Mutfwang maraba da shiga cikinta, bayan ficewa daga jam‘iyyar PDP.   Sakataren jam'iyyar Shitu Bamaiyi...

Tinubu ya jaddada wa Amurka kudurin kafa ‘yansandan jihohi a Nijeriya

Shugaban Nijeriya Bola Ahmed Tinubu ya sake jaddada kudurinsa na kafa 'yansandan jihohi a Nijeriya, yana mai cewa ya shaida hakan ga Amurka da sauran...

Mafi Shahara