DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Sojojin Nijeriya sun dakile harin ‘yan bindiga a jihar Borno

-

Rundunar sojin Nijeriya karkashin shirin ‘Operation Hadin Kai’ ta samu nasarar dakile wani hari da ‘yan ta’adda suka shirya kaddamarwa a yankin Bitta daga tsaunukan Mandara a jihar Borno.

 

Google search engine

Yayin gumurzun dai sojojin sun hallaka ‘yan ta’adda da dama kamar yadda jaridar Punch ta ruwaito.

 

Wata sanarwa da rundunar sojin ta fitar ta hannun Laftanar Kanal Sani Uba a shafinta na X, ta ce lamarin ya faru ne da misalin karfe 12 na daren Alhamis, inda sojojin suka gano motsin ‘yan ta’addan zuwa yankin.

 

Bayan fatattakar su, sanarwar ta kuma ce an samu nasarar kwato tarin makamai da sauran kayayyakin da ‘yan bindigar ke amfani da su wajen kaddamar da hare-hare kan al’umma.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

El-Rufai ya zargi gwamnatin Tinubu da hannu a yunƙurin sanya Kwankwaso cikin jerin takunkumin Amurka

Tsohon gwamnan Kaduna, Malam Nasir El-Rufai, ya yi zargin cewa gwamnatin Shugaba Bola Ahmed Tinubu na iya kasancewa a bayan yunƙurin dan Majalisar Dokokin Amurka,...

Shehu Sani ya karyata El-Rufai kan batun bacewar Dadiyata

Tsohon Sanatan Kaduna ta Tsakiya, Comrade Shehu Sani, ya karyata ikirarin tsohon gwamnan Kaduna, Malam Nasir El-Rufai, cewa Abubakar Idris wanda aka fi sani da...

Mafi Shahara