Shugaban Nijeriya Bola Ahmed Tinubu ya sake jaddada kudurinsa na kafa ‘yansandan jihohi a Nijeriya, yana mai cewa ya shaida hakan ga Amurka da sauran kawayen Nijeriya na Turai.
Shugaban ya bayyana haka ne a yayin taron jam’iyyar APC a Abuja, inda ya nanata bukatar gwamnoni su sakar wa kananan hukumomi ‘yancinsu na kashe kudade.
Tinubu ya ce wajibi ne a samar da jami’an don tabbatar da tsaron cikin gida da kuma inganta shugabanci, kamar yadda jaridar Punch ta ruwaito.



