DCL Hausa Radio
Kaitsaye

CDD ta horas da ‘yan jarida a Katsina kan yaki da labaran karya

-

Cibiyar bunkasa dimokradiyya ta CDD ta horas da ‘yan jarida a jihar Katsina kan aiki mai inganci.

CDD ta ce wannan na a wani yunkuri na karfafa kwarewa a aikin jarida tare da inganta rahoto kan ka’ida da gaskiya.

Google search engine

Jami’ar kula daga cibiyar ta CDD, Ms Chioma Valerie, ta bayyana cewa an tsara shirin ne domin bai wa ‘yan jarida dabarun da za su taimaka musu wajen yaki da labaran karya da kuma tafiyar da bayanai cikin kwarewa.
Ta ce daya daga cikin muhimman sakamakon bitar shi ne samar da ‘yan jarida da za su iya taimakawa wajen gina al’umma mai zaman lafiya da kwanciyar hankali, ta hanyar rahoto mai bin ka’idojin da’a da gaskiya.

A yayin bitar, an yi bayani dalla-dalla kan ma’anar tantance gaskiyar labari (fact-checking), manufarsa da muhimmancinsa, tare da bambance shi da tantance sahihancin bayani (verification), da yadda dukkan su ke taimakawa wajen samar da rahoto mai inganci.
Haka kuma, an yi gargadi kan illolin wallafa bayanan da ba a tantance ba, inda aka bayyana irin matsalolin da labaran karya ka iya jefa ‘yan jarida da al’umma a ciki.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

‘Yan bindiga sun halaka mutum 1,sun kuma mutane 5 a Zamfara

’Yan bindiga sun kai hari kauyen Fananawa da ke karamar hukumar Bukuyum ta jihar Zamfara, inda suka halaka mutum ɗaya tare da sace mutane biyar,...

‘Yan sanda sun kama wata mata a ake zargi da garkuwa da kanta

Rundunar ‘yan sandan jihar Legas ta cafke wata matar aure mai shekaru 26 tare da wani mutum mai shekaru 30, bisa zargin yin garkuwa da...

Mafi Shahara