Shugaban Majalisar Dattawa, Godswill Akpabio, ya garzaya Kotun Koli kan rikicin shari’a da ya biyo bayan dakatar da Sanatar Kogi ta Tsakiya, Natasha Akpoti-Uduaghan, bayan Kotun Ɗaukaka Ƙara da ke Abuja ta yi watsi da ƙarar da Gwamnatin Tarayya ta shigar.
Takardun kotu sun nuna cewa Kotun Ɗaukaka Ƙara ta ce ƙarar ba ta inganta ba saboda karya ƙa’idojin kotu, ciki har da amfani da rubutu da tazara da ba su dace ba, wuce adadin shafuka da aka kayyade, da kuma rashin neman izinin kotu.
Binciken jaridar PUNCH ya nuna cewa kotun ta yanke hukuncin ne bisa doka, ba bisa son rai ba.
Duk da haka, Akpabio ya nemi Kotun Koli ta soke hukuncin, matakin da ya jawo ce-ce-ku-ce a cikin jama’a, inda wasu masana shari’a ke ganin ba ruwan shugaban Majalisar Dattawa ya shiga shari’ar kai tsaye. Rikicin ya kuma kara fitowa fili sakamakon sabanin siyasa da ke tsakaninsa da Sanata Natasha, wadda ta shahara wajen sukar shugabancin Majalisar.



