DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Kasafin kudin Shugaba Tinubu na 2026 tarkon bashi ne ba gyara ba – Jam’iyyar ADC

-

Jam’iyyar ADC ta soki kudirin kasafin kuɗin shekarar 2026 da Shugaba Bola Tinubu ya gabatar, tana mai cewa kasafin tarkon bashi ne da aka lullube da sunan gyara, wanda ke dogaro da karɓar rance fiye da kima da kuma hasashen kudaden shiga da ba su da tabbas.

A cikin wata sanarwa da Sakataren Yada Labarai na ƙasa na jam’iyyar, Bolaji Abdullahi, ya fitar a ranar Litinin, ADC ta ce kasafin kuɗin na Naira tiriliyan 58.18 bai kawo sabon abu ba illa ci-gaba da abin da ta kira sakacin tafiyar da kuɗin gwamnati, inda aka gabatar da irin kasafin shekarun 2024 da 2025 da ba a aiwatar da yawansu ba.

Google search engine

Jam’iyyar ta ce duk da ikirarin gwamnati na kashe Naira tiriliyan 25.68 kan ayyukan raya ƙasa, gibin kasafin da ya kai Naira tiriliyan 23.85 na nuna cewa kusan dukkan ayyukan za a yi su ne da bashi mai tsada, tana mai gargadin cewa hakan na iya jefa Nijeriya cikin ƙarin matsin tattalin arziki da ɗaure makomar ’ya’ya masu zuwa.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Har yanzu bamu kammala bincike ba shiyasa bamu gurfanar da El-rufa’i a gaban kotu ba – EFCC

Hukumar EFCC, mai yaki a cin hanci da rashawa a Nijeriya ta bayyana dalilin da ya sa har yanzu ba ta kai tsohon gwamnan Kaduna,...

Wanene sabon Shugaban Rundunar ‘Yan Sandan Nijeriya, Olatunji Disu?

AIG Olatunji Disu ya kasance gogaggen jami’i wanda aka nada don jagorantar rundunar 'yan sandan kasar a matsayin IGP na 23. A cewar fadar shugaban...

Mafi Shahara