DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Kasafin kudin Shugaba Tinubu na 2026 tarkon bashi ne ba gyara ba – Jam’iyyar ADC

-

Jam’iyyar ADC ta soki kudirin kasafin kuɗin shekarar 2026 da Shugaba Bola Tinubu ya gabatar, tana mai cewa kasafin tarkon bashi ne da aka lullube da sunan gyara, wanda ke dogaro da karɓar rance fiye da kima da kuma hasashen kudaden shiga da ba su da tabbas.

A cikin wata sanarwa da Sakataren Yada Labarai na ƙasa na jam’iyyar, Bolaji Abdullahi, ya fitar a ranar Litinin, ADC ta ce kasafin kuɗin na Naira tiriliyan 58.18 bai kawo sabon abu ba illa ci-gaba da abin da ta kira sakacin tafiyar da kuɗin gwamnati, inda aka gabatar da irin kasafin shekarun 2024 da 2025 da ba a aiwatar da yawansu ba.

Google search engine

Jam’iyyar ta ce duk da ikirarin gwamnati na kashe Naira tiriliyan 25.68 kan ayyukan raya ƙasa, gibin kasafin da ya kai Naira tiriliyan 23.85 na nuna cewa kusan dukkan ayyukan za a yi su ne da bashi mai tsada, tana mai gargadin cewa hakan na iya jefa Nijeriya cikin ƙarin matsin tattalin arziki da ɗaure makomar ’ya’ya masu zuwa.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

An fitar da jihohi 4 a Gasar Kokawar Nijar ta 2025

Kwana na uku da fara gasar kokawar gargajiya a Nijar tuni an yi waje da jihohi hudu daga cikin takwas na kasar daga jerin wanda...

Ya kamata a canza salon yadda ake yakar ‘yan bindiga a Nijeriya

Daga: Farfesa Usman Yusuf Litinin : 22 Disamba 2025 Ban taɓa gudu ko ja da baya ba ko nuna wata fargaba wajen bayyana matsayina a kan yaƙin...

Mafi Shahara