DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Kotu ta amince da a bayar da belin Abubakar Malami 

-

Babbar Kotu a Birnin Tarayya Abuja ta amince da belin tsohon ministan shari’ar Nijeriya Abubakar Malami, SAN, wanda ke fuskantar  zarge-zargen cin hanci daga hukumar EFCC.

Umurnin kotun ya fito ne a ranar 23 ga Disamba, 2025, inda mai shari’a Justice Bello Kawu ya yanke hukuncin amincewa da belin Malami bayan sauraron roƙon gaggawa (motion ex-parte) da lauyansa ya shigar, tare da la’akari da hujjar da aka gabatar a gaban kotu.

Google search engine

Kotun ta umurci Malami da ya miƙa fasfo dinsa na ƙasashen waje, tare da cika sharuddan beli kamar yadda EFCC ta tanada tun da farko. Daga cikin sharuddan akwai bayar da masu tsayawa masa  mutum biyu, ciki har da Darakta Janar na wata hukumar shari’a da kuma ɗan majalisar wakilai mai wakiltar mazabar Augie/Argungu.

Har ila yau, kotun ta amince da sake farfaɗo da sharuddan belin da aka cika a ranar 28 ga Nuwamba, 2025, tare da dage sauraron shari’ar zuwa ranar 5 ga Janairu, 2026.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Peter Obi ya bukaci matasa da su nuna kauna da kishin Nijeriya albarkacin ranar masoya

Tsohon ɗan takarar shugaban Nijeriya, Peter Obi, ya bukaci ’yan Nijeriya musamman matasa su yi bikin ranar masoya ta Valentine cikin nuna kishin ƙasa da...

Nijeriya na da damar jagorantar Afirka ta zama babbar nahiya a duniya – António Guterres

Sakatare-Janar na Majalisar Dinkin Duniya, António Guterres, ya bukaci Nijeriya ta jagoranci Afirka wajen neman sauyi a tsarin duniya, yana mai cewa ƙasar na da...

Mafi Shahara