Kocin Super Eagles, Eric Chelle, ya bayyana cewa har yanzu Nijeriya na da damar ingantawa a gasar Cin Kofin Afirka ta 2025 duk da nasarar 2–1 da suka samu a kan Tanzania a ranar Talata, rahoton PUNCH Sports Extra.
A wasan da aka buga a Complexe Sportif de Fès, Morocco, Semi Ajayi ya zura kwallo bayan minti 36 daga bugun kusurwar Alex Iwobi, amma Tanzania ta daidaita wasan da Charles M’Mombwa kafin Ademola Lookman ya sake ba Nijeriya jagoranci. Duk da haka, ‘yan wasan Chelle sun nuna kwarin gwiwa a don kare nasarar.
Chelle ya yi sharhi kan wasan yana mai cewa, “Dole ne mu nazarci wannan nasara saboda mun yi abubuwa da dama a rabin farko wajen hare-haren kwallaye. Amma a rabin na biyu, mun baiwa Tanzania damar dawowa cikin wasan. Mun yi kuskure biyu.”
Ya ƙara da cewa, “Tabbas muna farin ciki da samun maki uku, amma a AFCON, abu mafi muhimmanci shi ne mu cigaba da inganta kowane wasa.



