Ofishin Abubakar Malami, SAN, ya yi tir da yadda EFCC ta ki bin umarnin kotun FCT Abuja na a saki Malami bayan ya cika sharuddan da aka tsara a ranar 23 Disamba, 2025.
A cikin wata sanarwar da ofishin ya fitar, ta ce EFCC ta cigaba da tsare shi fiye da kwanaki 14 ba tare da gurfanar da shi a kotu ba, yayin da take amfani da kafafen watsa labarai wajen yada labarai don lalata masa suna.
Ofishin ya yi kira ga kotu da hukumomin sa ido da su ɗauki mataki cikin gaggawa, sannan ya jaddada cewa babu wata hukuma da ta fi karfin doka.



