DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Hukumar Tarayyar Turai ta yi Allah-wadai da haramta biza da Amurka ta yi wa wasu Turawa

-

Tarayyar Turai, tare da ƙasashen Faransa da Jamus, sun yi kakkausar suka ga matakin Amurka na haramta biza ga wasu ’yan Turai da ke yaki da kalaman ƙiyayya da yaɗa ƙarya a kafafen intanet, suna mai cewa matakin ba shi da hujja.

Gwamnatin Shugaban Amurka Donald Trump ta saka haramcin ne a ranar Talata kan ’yan Turai biyar, ciki har da tsohon kwamishinan EU ɗan Faransa, Thierry Breton, bisa zargin takaita ’yancin faɗar albarkacin baki da kuma tsaurara dokoki kan manyan kamfanonin fasaha na Amurka.

Google search engine

Hukumar Tarayyar Turai ta ce tana yin Allah-wadai da matakin, tare da jaddada cewa ’yancin faɗar albarkacin baki muhimmiyar ƙima ce da Turai da Amurka ke rabawa. Ta kuma yi gargaɗin cewa za ta iya ɗaukar mataki cikin gaggawa.

Rahoton Reuters ya ce lamarin na iya ƙara rarrabuwar kai tsakanin Amurka da wasu ƙasashen Turai kan batutuwan tsaro, kasuwanci, siyasa da dokokin kafafen sada zumunta, musamman bayan EU ta ci tarar dandalin X na Elon Musk kan karya wasu dokoki a intanet.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Shugaba Tinubu ya yi kira ga hadin kai da hakuri a tsakanin addinai a cikin sakon taya murnar bikin Kirsimeti

Shugaban Nijeriya Bola Tinubu ya yi kira ga ’yan Nijeriya da su rungumi haɗin kai, juriya da zaman lafiya tsakanin mabiya addinai, yana mai cewa...

Akwai bukatar dole sai ‘yan kwallon Super Eagles sun inganta wasansu matukar suna son nasara – Eric Chelle

Kocin Super Eagles, Eric Chelle, ya bayyana cewa har yanzu Nijeriya na da damar ingantawa a gasar Cin Kofin Afirka ta 2025 duk da nasarar...

Mafi Shahara