Mawaki Davido, ya sanar da shirin sa na shiga jam’iyyar Accord, inda zai bi sawun kawunsa, Gwamna Ademola Adeleke na Osun.
Mawakin ya ce zai kasance a Osogbo a ranar Laraba domin karɓar katin zama mamba na jam’iyyar.
Wannan lamari ya biyo bayan Gwamna Adeleke da ya sanar da barin PDP zuwa jam’iyyar Accord kafin zaɓen gwamna na 2026.
Shirin Davido ya jawo ce-ce-ku-ce a shafukan sada zumunta, inda ake lura da yadda shahararrun mutane ke shiga harkokin siyasa a Nijeriya.



