DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Shugaba Tinubu ya yi kira ga hadin kai da hakuri a tsakanin addinai a cikin sakon taya murnar bikin Kirsimeti

-

Shugaban Nijeriya Bola Tinubu ya yi kira ga ’yan Nijeriya da su rungumi haɗin kai, juriya da zaman lafiya tsakanin mabiya addinai, yana mai cewa gwamnatinsa za ta cigaba da kare ’yanci da lafiyar kowa ba tare da la’akari da addini ba.

Tinubu ya bayyana haka ne a saƙon taya murnar Kirsimeti na shekarar 2025 da ya fitar a ranar Laraba, inda ya taya Kiristoci a Nijeriya da sauran sassan duniya murna, yana mai cewa Kirsimeti lokaci ne na tunani kan haihuwar Annabi Isa Almasihu da saƙon zaman lafiya, ƙauna da fata.

Google search engine

Tinubu ya ce saƙon Almasihu a matsayin jagoran zaman lafiya ya dace sosai a wannan lokaci da Nijeriya ke fuskantar ƙalubale iri-iri, yana mai tabbatar da cewa gwamnatinsa na jajircewa wajen tabbatar da ’yancin addini da kare jama’a daga duk wani nau’in tashin hankali.

Haka kuma ya yaba da gudummawar da Kiristoci ke bayarwa wajen ci-gaban Nijeriya, yana mai kira da a yi amfani da lokacin Kirsimeti wajen ƙarfafa zaman lafiya da fahimtar juna a tsakanin ’yan ƙasa.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Hukumar Tarayyar Turai ta yi Allah-wadai da haramta biza da Amurka ta yi wa wasu Turawa

Tarayyar Turai, tare da ƙasashen Faransa da Jamus, sun yi kakkausar suka ga matakin Amurka na haramta biza ga wasu ’yan Turai da ke yaki...

Akwai bukatar dole sai ‘yan kwallon Super Eagles sun inganta wasansu matukar suna son nasara – Eric Chelle

Kocin Super Eagles, Eric Chelle, ya bayyana cewa har yanzu Nijeriya na da damar ingantawa a gasar Cin Kofin Afirka ta 2025 duk da nasarar...

Mafi Shahara